Sojojinmu ne ke iko da muhimman wurare - shugaban Sudan

 


Janar Abdel Fattah al-Burhan, jagoran Sudan kuma babban hafsan hafsoshin sojin ƙasar ya musanta iƙirarin rundunar jami'ai masu kayan sarki ta RSF, cewa dakarunta ne ke iko da fadar shugaban ƙasa da hedkwatar sojoji da kuma filin jirgin sama.

A wani saƙon waya da aka naɗa lokacin hira da gidan talbijin na Al Jazeera, Janar al-Burhan ya dage kan cewa dakarunsa ne har yanzu ke da iko.

Ana ci gaba da samun rahotanni masu cin karo da juna game da abin da ke faruwa a tsawon wannan rana kan taƙamaimai wane ne ke iko da muhimman wurare a birnin Khartoum.

BBC

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki