’Yan Matan Chibok’ 2 Sun Gudo Daga Hannun Boko Haram


 Karin mutum biyu daga cikin daliban Makarantar Sakandaren ’Yan Mata da ke Chibok a Jihar Borno sun gudo daga hannun mayakan Boko Haram da suka sace su shekaru tara da suka gabata.

Majiyoyin tsaro da mazauna Jihar Borno sun shaida wa wakilinmu cewa matan su biyu sun samu tserewa a dalilin tsananta luguden wuta da sojoji suke yi a kan sansanonin kungiyar da ke Dajin Sambisa

Wata majiyar tsaro ta ce daliban da suka gudo su ne Hauwa Mutah da kuma Esther Markus.

Ta bayyana cewa, “Daya daga cikinsu ’yar kauyen Chibok ce, dayar kuma ’yar kauyen Dzilang ce.”

Mako biyu da suka gabata, rundubar soji ta Operation Hadinkai da ke yaki da kungiyar, ta bayyana cewa akwai saura mutum 98 daga cikin Daliban Chibok a hannun kungiyar.

Kwamandan Sashen Lelen Asiri na rundunar, Kanar Obinna Ezuipke ya ce, “Daga cikin Daliban Chibok 276 da aka sace, 57 sun tsere a 2014, an sako 107 a 2018.

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki