Ganduje Ya Yi Wa Fursunoni Sama Da Dubu Hudu Afuwa A Cikin Shekaru Takwas


 Gwamnan jihar Kano Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana cewa gwamnatinsa ta yi afuwa ga fursunoni dubu hudu da goma sha uku a cikin shekaru takwas a fadin gidajen gyaran hali na Kano.

 Haka kuma a cikin shekaru takwas gwamnatinmu ta biyan tara da diyya ga fursunonin da suka kai naira miliyan hudu da dubu dari tara da arba’in da tara.

 Gwamnan wanda ya sami wakilcin mataimakinsa Dr. Nasiru Yusuf Gawuna ya bayyana haka a lokacin da ya yi afuwa ga fursunoni 43 da suka aikata laifuka daban-daban kuma suke zaune a gidan yari, a yayin bikin karamar Sallah da aka yi a gidan yari na Goron Dutse.

Ganduje ya jaddada cewa ’yanci shi ne komai na rayuwar dan Adam, ya yi kira ga fursunonin da aka yi wa afuwar da su nuna kyawawan halaye a duk inda suka samu kansu a cikin al’umma.


A jawabinsa Kwanturola na hukumar gyaran jiki a jihar kano, Suleiman Muhammad Inuwa ya bayyana cewa matakin da gwamnatin jihar Kano ta dauka na yin afuwa ga fursunonin da biyan tara, diyya ya taimaka wajen rage cunkoso da kuma samar da zaman lafiya a  gidajen gyaran hali dake kano.

 Ya kuma yi kira ga sauran jihohi da su yi koyi da wannan matakin sannan kuma ya bukaci wadanda suka amfana da su kasance jakadu nagari  su kasance masu bin doka da oda ta hanyar nuna kyawawan halaye.
 
A sanarwar da Sakataren yada labaran mataimakin gwamna Hassan Musa Fagge ya aikowa kadaura24, yace a nasa bangaren, Shugaban kwamitin yiwa fursunoni afuwa na jihar kano Abdullahi Garba Rano, ya mika godiyarsa ga Gwamnan bisa amfani da damar da kundin tsarin mulki ya ba shi na sakin fursunonin don.
KADAURA24 

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki