Shugaba Biden ya bayyana aniyar sake tsayawa takara

 


Shugaban Amurka Joe Biden ya sanar da cewa zai sake tsayawa takara a zaɓen shekara ta 2024, inda mai yiwuwa ya sake takara da Donald Trump.

An yi tsammanin jam'iyyar Democrat za ta sake neman wa'adin mulki na biyu tsawon shekara huɗu tare da ƙaddamar da yaƙin neman zaɓensa a wani bidiyo ranar Talata.

Ya ce wannan muhimmin lokaci ne da zai sake bayyana aniyrasa ta sake neman mulkin Amurka.

Mataimakiyar shugaban ƙasar Kamala Harris, mai shekaru 58, ita ma ta nuna aniyar sake zama abokin takararsa.

Mista Biden, mai shekaru 80, shi ne shugaban ƙasa mafi tsufa a tarihin Amurka, kuma da alama zai fuskanci tambayoyi kan shekarunsa a tsawon lokacin yakin neman zaɓe.

Zai kasance mai shekara 86 bayan kammala wa'adinsa na biyu a mulkii cikin shekara ta 2029.

BBC

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki