Search This Blog

Wednesday, 14 June 2023

Majalisar Dokoki Ta Kano Ta Amince Da Mutum 20 Da Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Mika Mata Don Nadasu Masu Bashi Shawara Na Musamman

Majalisar dokokin jihar Kano ta amince da nadin mukamai na musamman guda ashirin da gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi.

Jaridar Daily News 24 ta ruwaito cewa ta Sahalewa Gwamnan ne a yayin wani zama da shugaban majalisar, Ismail Jibrin Falgore ya jagoranta bisa tsari na 196/2 na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya.

Sanarwar da Babban Sakataren Yada Labarai na Majalisar, Uba Abdullahi ya fitar ta ce amincewar ta biyo bayan wasikar da Gwamnan ya aike wa majalisar na neman nadin wanda aka tattauna a gaban zauren majalisar tare da cimma matsaya.

Majalisar ta dage zamanta zuwa ranar 19 ga watan Yuni, 2023 a wani kudiri da shugaban masu rinjaye Hon Lawan Husaini na mazabar Dala ya gabatar kuma shugaban marasa rinjaye, Labaran Abdul Madari na mazabar Warawa ya mara masa baya.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...