Majalisar Dokoki Ta Kano Ta Amince Da Mutum 20 Da Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Mika Mata Don Nadasu Masu Bashi Shawara Na Musamman

Majalisar dokokin jihar Kano ta amince da nadin mukamai na musamman guda ashirin da gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi.

Jaridar Daily News 24 ta ruwaito cewa ta Sahalewa Gwamnan ne a yayin wani zama da shugaban majalisar, Ismail Jibrin Falgore ya jagoranta bisa tsari na 196/2 na kundin tsarin mulkin tarayyar Najeriya.

Sanarwar da Babban Sakataren Yada Labarai na Majalisar, Uba Abdullahi ya fitar ta ce amincewar ta biyo bayan wasikar da Gwamnan ya aike wa majalisar na neman nadin wanda aka tattauna a gaban zauren majalisar tare da cimma matsaya.

Majalisar ta dage zamanta zuwa ranar 19 ga watan Yuni, 2023 a wani kudiri da shugaban masu rinjaye Hon Lawan Husaini na mazabar Dala ya gabatar kuma shugaban marasa rinjaye, Labaran Abdul Madari na mazabar Warawa ya mara masa baya.

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki