Gwamnan Kano ya taya al'ummar Kano murnar bukukuwan Sallah

Gwamna Abba Kabir Yusuf ya taya al'ummar Kano murnar bikin Sallah.

Gwamnan a cikin sakon da mai rikon mukamin babban sakataren yada labaransa, Hisham Habib ya sanyawa hannu, Ta Ce Gwamnan ya bukaci al’ummar musulmi da su daure su kasance masu taimakon juna.


Gwamna Kabir ya yi wa alhazan kasa mai tsarki addu’ar Allah ya kai su gida lafiya.


Ya kuma jaddada aniyar gwamnatinsa na tallafawa harkokin kiwon lafiya, ilimi, kare muhalli da kuma noma.


Ya ce gwamnati za ta ci gaba da jaddada jin dadin ‘yan kasa


Mai Martaba Sarkin Kano Alh Aminu Ado wanda ya tarbi Gwamna Abba Kabir a Gidan Shetima wanda ya bukaci al’ummar Kano da su fito a kidaya su a kidayar jama’a na gaba domin tabbatar da matsayin Kano a matsayin jiha mafi yawan al’umma.


Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki