Gwamnan Kano ya nada fitaccen Dan Jarida, Ibrahim Garba Shu'aibu A Matsayin Babban Sakataren Yada Labaran Mataimakinsa

Gwamna Abba Kabir yusuf ya amince da nadin Ibrahim Garba Shu'aibu a matsayin babban sakataren yada labaran mataimakinsa Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo.

A sanarwar da babban sakataren yada labaran Gwamna, Sunusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, tace Ibrahim wanda ya kammala karatun wallafe-wallafen Turanci daga Jami'ar Bayero, Kano. Kafin nadin nasa, ya kasance wakilin Jaridar Thisday a Kano kuma shugaban kungiyar wakilai masu daukar Rahotannin Kamfanonin jaridu na Kano.

Sauran wadanda aka sanar da nadin nasu sun hada da :

2. Lawan Adamu Mika, Babban mataimaki na musamman, harkokin Karbar baki 

3. Abubakar Tijjani Kura, Babban mataimaki na musamman kan harkokin gudanarwa

4. Muhammad Garba Gwarzo, mataimaki na musamman, al'amuran siyasa

5. Abubakar Salisu Mijinawa, mataimaki na musamman na harkokin cikin gida

6. Usman Nura Geto, mataikai kan harkokin gudanarwa

7. Hamza Ahmad Telata Mata, mataimaki kan harkar daukar hoto

Sanarwar ta bayyana cewa dukkanin nadin sun fara aiki ne nan take 

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki