Yanzu-Yanzu: Gwamnatin Tarayya Ta Sanar Da Ranakun Hutu

Gwamnatin tarayya ta ayyana ranakun Talata da Laraba 9 da 10 ga Afrilu, 2024 a matsayin ranakun hutu domin bukukuwan Sallah.

Ministan harkokin cikin gida Olubunmi Tunji-Ojo ne ya bayyana hakan a wata sanarwa da babban sakataren ma’aikatar, Aishetu Ndayako ya fitar ranar Lahadi.

Ministan ya taya daukacin al’ummar musulmi murnar kammala azumin watan Ramadan mai alfarma.


Tunji-Ojo ya yi kira gare su da su yi koyi da kyawawan dabi’u da suka hada da kyautatawa, soyayya, hakuri, zaman lafiya, makwabtaka, tausayi, kamar yadda Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama ya bayar da misali da shi.
(SOLACEBASE)

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki