Hajjin 2024: Tawagar Amirul-Hajjin Bauchi Ta Gudanar Da Taron Kaddamar Da Aikin Hajji Tare Da Tabbatar Da Inganta Aikin Hajji.

Kwamitin Amirul-Hajj na jihar Bauchi mai mutane goma sha biyar ya bayyana aniyarsa na ganin an samar da isasshen jin dadin alhazan jihar da ke shirin zuwa kasar Saudiyya.

A sanarwar da sakataren tawagar Amirul Hajj din, Mohammed Haruna Barde ya sanyawa hannu, yace Amirul-Hajj Alhaji Usman Bilyaminu Othman ya yi wannan alkawarin ne yayin taron kaddamar da kwamitin da aka gudanar a gidan gwamnati Bauchi.

Alhaji Usman Bilyaminu Othman wanda shi ne Sarkin Dass ya lura cewa kwamitin zai yi nazari kan rahoton aikin Hajjin bara da nufin samar da mafita ga kalubalen da aka gano.

Da yake godiya ga Gwamna Bala Mohammed bisa amincewar da aka basu, Amirul-Hajj ya bukaci mambobin kwamitin da su yi aiki tare domin cimma burin da ake so.

A nasa bangaren, Sakataren zartarwa na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jiha Imam Abdurrahman Ibrahim Idris ya ce hukumar ta yi isassun shirye-shirye domin tabbatar da gudanar da atisayen da ba a taba gani ba.
A cewarsa tare da goyon bayan Gwamna Bala Mohammed, Bauchi ta samu nasarar yiwa maniyyata aikin hajji sama da dubu biyu da dari shidda rijista wanda ya zarce na sauran jihohin kasar nan.

Mohammed Haruna Barde Dcos.
Sakataren tawagar Amirul Hajj.

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki