DA DUMI-DUMI: Gwamnatin Kano Ta Shigar Da Karar Tsohon Gwamna Abdullahi Ganduje, Matarsa, Hafsat Wasu Mutane 6 A Kotu Akan Zargin Cin Hanci Da Rashawa

Gwamnatin jihar Kano ta shigar da karar tsohon gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje, matarsa Hafsat Umar, Umar Abdullahi Umar da wasu mutane biyar a gaban kotu bisa zarge-zarge 8 da suka hada da cin hanci da rashawa da karkatar da wasu kudade da suka shafi biliyoyin naira.



Wannan yana kunshe ne a cikin takardar tuhuma mai kwanan wata 3 ga Afrilu, 2024 tare da jerin shaidu 15 da aka makala.



SOLACEBASE ta ruwaito cewa sauran wadanda ake kara a karar sun hada da Abdullahi Umar Ganduje, Hafsat Umar, Abubakar Bawuro, Umar Abdullahi Umar, Jibrilla Muhammad, Lamash Properties Ltd, Safari Textiles Ltd da Lesage General Enterprises.

, Cikakken labarin zai zo muku nan gaba kadan 

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki