Gwamnatin Kano Ta Yi Alkawarin Mayar Da Karin Albashin Shekara-Shekara Ga Ma'aikata

Gwamnatin jihar Kano karkashin Alhaji Abba Kabir Yusuf, ta yi alkawarin dawo da biyan  karin kudaden da ake biyan ma’aikata a duk shekara, nan take bayan an gudanar da aikin tantance ma’aikata da tantance bayanan da aka yi.

A sanarwar da daraktan wayar da kan al'uma na hukumar, Bashir Habib Yahaya ya sanyawa hannu, yace Babban Akanta Janar na Jihar Kano, Alhaji Abdulkadir Abdulsalam ne ya bayyana hakan a lokacin wani taro da masu ruwa da tsaki kan yadda ake gudanar da aikin tantancewa da daukar bayanan ma'aikatan 

Alhaji Abdulkadir ya bayyana cewa tun bayan amincewar majalisar zartarwa ta jiha na gudanar da aikin da kuma abin da gwamnan jihar Alhaji Abba Kabir Yusuf ya kaddamar, nan da nan aka fara shirye-shirye tare da kara zage damtse don ganin an gudanar da aikin.

Ya ci gaba da cewa, gwamnatin jihar ta amince da kwamitoci biyu na dindindin kan aikin biyan albashin ma’aikata a matakin jiha da kananan hukumomi baya ga ‘yan fansho.

A nasa jawabin kwamishinan kudi da ci gaban tattalin arzikin jihar Alhaji Ibrahim Jibrin Fagge ya bayyana cewa gwamnatin jihar ta kaddamar da wannan aikin ne domin tantance adadin ma’aikatan ta domin kaucewa zurarewar kudaden jama’a.

A nasa jawabin shugaban kwamitin riko na biyan albashin ma’aikata na jiha, Alhaji Faruk Umar Ibrahim ya bayyana wasu ayyuka da shawarwarin kwamitin na sa kan yadda ya kamata a gudanar da aikin.

Ya ci gaba da cewa, kwamitocin biyu a shirye suke su karbi shawarwari da lura wadanda za su yi matukar amfani wajen gudanar da atisayen cikin nasara.

Tun da farko, a nasa jawabin, sakataren gwamnatin jihar (SSG), Dakta Abdullahi Baffa Bichi, ya umarci kwamitocin a maimakon rubuta lambar tantance bankin (BVN) a kan fom din a lokacin tantancewa.



Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki