Mataimakin Gwamnan Kano Ya Umarci Shugabannin Kwamitin Riko Da Su Ci Gaba Da Zama A Kananan Hukumominsu

Mataimakin Gwamnan Jihar Kano, Kwamared Aminu Abdussalam Gwarzo, ya umurci shugabannin kwamitocin riko na kananan hukumomi 44 da su zauna ko su koma kananan hukumomin da aka nadasu.

Gwarzo ya bayar da umarnin ne a jiya (Asabar) yayin da yake karbar sama da mutane 1000 da suka sauya sheka daga jam’iyyar APC zuwa New Nigerian Peoples Party (NNPP) daga Shanono a gidan gwamnati dake Kano.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da mai magana da yawun mataimakin gwamnan, Ibrahim Garba Shuaibu ya raba wa manema labarai a ranar Lahadi.

Mataimakin Gwamna Gwarzo, wanda kuma yake rike da mukamin kwamishinan kananan hukumomi da masarautu, ya jaddada mahimmancin shugabannin kwamitocin riko su kasance cikin shiri a kananan hukumomin da aka nadasu.

Ya umarce su da su tafi zuwa majalisunsun kananan hukumominsu tare da fara ayyuka masu tasiri a sassa masu mahimmanci kamar kiwon lafiya, ilimi, da samar da ruwa.

Mataimakin gwamnan ya yi gargadin cewa gwamnatin jihar ba za ta amince da shugabancin wanda ba ya zama a yankinsa, ya kuma jaddada bukatar shugabannin su zauna a tsakanin al’ummar da suke wakilta.

Don tabbatar da bin ka’ida, Gwarzo ya sanar da shirin kai ziyarar ba-zata zuwa kananan hukumomi daban-daban domin tantance sadaukarwar da shugabannin kwamitin riko suka yi a ayyukan da aka ba su.

Duk da wannan umarni, mataimakin gwamnan ya tabbatar wa da jama’a kan kudirin Gwamna Abba Kabir Yusuf na aiwatar da shirye-shiryen da suka amfana da dukkanin yankunan jihar Kano.

A karshe ya bukaci jama’a su ci gaba da marawa gwamnati baya domin ganin an samu ci gaba da wadata.


Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki