Search This Blog

Sunday, 27 August 2023

Kada Wanda Ya Kafa Allunan Taya Ni Murnar Zama Minista – Wike

 


Ministan Abuja, Nyesom Wike, ya hana karkafa duk wasu allunan talla da nufin taya shi murnar zama Minista.

A cikin wata sanarwa da Daraktan Yada Labarai na ma’aikatar, Anthony Ogunleye, Wike ya ce ya yanke shawarar daukar matakin ne saboda nuna kishin kasa da kuma mayar da hankali wajen aikin da Tinubu ya sa shi.

Sanarwar ta ce Ministan ya gode da fatan alherin, amma ya bukaci a dakatar da amfani da irin wadannan allunan tallan.

Wike ya ce babban burinsa shi ne ya bunkasa Abuja ta yadda mazauna cikinta za su ji dadin zamanta a zamanin mulkinsa.

Ya kuma ce ya yana matukar girmamawa da kuma mutunta bukatun mazauna birnin tare da jajircewa wajen ganin ya biya musu su.
AMINIYA

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...