Jami’ar Bayero ta sanya hannu kan yarjejeniyar fahimtar juna da Gidan Zoo

Da yake jawabi yayin bikin wanda ya gudana a harabar gidan adana namun dajin, shugaban jami’ar, Farfesa Sagir Adamu Abbas, ya ce tun kafin wannan sabon ci gaba akwai dangantaka tsakanin bangarorin biyu, inda ya kara da cewa jami’ar Bayero ta kasance tana zuwa  Lambun Zoo don bayar da shawarwarin shawarwari akan dabbobi

Yace yarjejeniyar ta shafi bunkasa Samar da allurar rigakafin dabbobi da musayar ma'aikata 

Mataimakin Shugaban Jami’ar ya kuma bayyana cewa Jami’ar daga lokaci zuwa lokaci ta kan shigo domin gabatar da taron karawa juna sani da mu’amala tsakanin cibiyar da ma’aikatan Hukumar.

Farfesa Sagir Adamu Abbas ya bayyana cewa a ko da yaushe Jami’ar a shirye take don kara yin hadin gwiwa a fannonin musayar ma’aikata, alluran rigakafi da kuma fannin dazuzzuka.

Ya kuma bayyana cewa bayan taron, cibiyar za ta fara fadada fannin ta hanyar gayyatar shugaban noma da ya shigo domin gudanar da aikin gandun daji sannan sauran sassan da abin ya shafa za su shigo domin samar da alluran rigakafin.

Shugaban jami’ar ya ci gaba da cewa, wurin ya kasance wata kadara ce ga gwamnatin jiha kuma tushen ilimi wanda idan aka kiyaye al’umma za su amfana da shi.

Tun da farko, Manajan Darakta na Gidan Zoo, Sadiq Kura Muhammed, ya bibiyi tarihin gidan adana namun dajin da ya ce tsohon gwamnan Kano, kwamishinan ‘yan sanda Audu Bako ne ya kafa a shekarar 1971.

Sadik Kura Muhammed ya ce babban burin samar da wurin a lokacin, shi ne na kiyayewa, ilimi da kuma nishadi inda ya ce babban abin da ake hadawa da shi shi ne namun daji da yin bincike da yin alluran rigakafin kare namun daji da kuma fannin raya jarin dan Adam da dai sauran fannoni

Manajan daraktan ya ci gaba da bayyana cewa, sauran bangarorin yarjejeniyar  cibiyar za ta tura wasu masu bincikenta zuwa lambun, yayin da gidan namun daji kuma za su iya tura wasu ma’aikatanta zuwa jami’ar domin su samu karin ilimi a kan kiyaye namun daji da suke da su.

Daga nan sai ya yi kira ga shugaban jami’ar da ya sanya hannu kan wata yarjejeniyar fahimtar juna tsakanin bangarorin biyu a fannin dazuzzuka kan yadda za a kiyaye da inganta illolin da suke da shi a dajin Falgore.

Muhimman abubuwan da aka gudanar a yayin taron sun hada da sanya hannu da kowanne bangare ya yi kan takardar yarjejeniyar fahimtar junar 

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki