Masu Garkuwa Da Mutane Sun Sace Jami'in Alhazai A Kano

A daren jiya Asabar ne, wasu mutane da ake zargin masu garkuwa da mutane ne,suka je har gida suka tafi da Jami'in Alhazai na Karamar Hukumar Bebeji

Alhaji Sagiru Umar Kofa, ya kasance babban hadimi ga zababben dan majalisar tarayya mai wakiltar kananan hukumomin Kiru da Bebeji, Abdulmumin Jibrin Kofa 

Majiyarmu ta tabbatar mana cewa masu garkuwa wadanda suka shiga gidan Sagiru Kofa su biyar, an tabbatar cewa wasu daga cikinsu na dauke da bindiga

A halin yanzu dai tuni jami'an 'yan sanda sun dukufa domin gano inda masu garkuwar suka yi da shi don ƙoƙarin kubutar da shi 

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki