Kotun Koli ta umarci Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta cire sunan tsohon Gwamnan Kano, Sanata Ibrahim Shekarau, a matsayin wanda ya ci zaben Sanatan Kano ta Tsakiya.
Kotun ta umarci INEC ta maye gurbin Shekarau da sunan Rufai Hanga a matsayin halastaccen wanda ya ci zaben kujerar a karkashin Jam’iyyar NNPP.
Ta kuma tabbatar da hukuncin Kotun Daukaka Kara da ta tabbatar da Rufai Hanga a matsayin halastaccen dan takarar NNPP a zaben da aka gudanar ranar 25 ga watan Maris.
INEC dai ta bayyana Shekarau a matsayin wanda ya ci zaben duk kuwa da cewa ya sauya sheka daga NNPP zuwa PDP kuma ya sanar da cewa ya janye daga takarar.
AMINIYA
