Search This Blog

Monday, 20 March 2023

Sanata Uba Sani Ya Samu Nasarar Zama Gwamnan Kaduna

An bayyana dan takarar jam’iyyar All Progressives Congress (APC) Sanata Uba Sani a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan jihar Kaduna a shekarar 2023.



Jami’in kula da masu kada kuri’a na jihar Kaduna kuma mataimakin shugaban jami’ar Usman Dan Fodio Sokoto, Farfesa Lawal Suleiman Bilbis ne ya bayyana shi a matsayin wanda ya lashe zaben.



Sani ya samu kuri'u 730,002 inda ya kayar da babban abokin hamayyarsa Isa Ashiru na jam'iyyar PDP wanda ya samu kuri'u 719,196.


Dan takarar jam’iyyar Labour Party (LP), Jonathan Asake ya zo na uku mai nisa bayan ya samu kuri’u 58,283 yayin da dan takarar jam’iyyar New Nigeria Peoples Party (NNPP), Suleiman Hunkuyi ya samu kuri’u 21,405.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Head of Service Urges Civil Servants to Uphold Ethical Conduct

The Head of Service, Kano State, has called on civil servants to strictly adhere to the Civil Service ethical code and show grea...