Buhari Ya Je Maiduguri Domin Jajantawa 'Yan Kasuwar Monday Market

Shugaban Kasa Muhamamdu Buhari ya isa Jihar Borno, domin jajanta wa ’yan kasuwar da iftila’in gobora ta shafa a Kasuwar Monday da ke Maiduguri.

An wayi gari ranar Lahadi a Maiduguri da gobarar, wadda ta lakume dubban shaguna a kasuwar, wadda ita ce mafi girma a Jihar Borno da ma yankin Arewa maso Gabashin Najeriya.

’Yan sanda na ci gaba da tsare Ali Madaki kan daukar bindiga a yakin neman zabe

Ana sa ran a yayin ziyarar ta ranar Alhamis, Buhari zai je Fadar Shehun Borno, inda zai jajanta wa ’yan kasuwar da suka yi asarar dukiyoyinsu a gobarar ta ranar Lahadi.

Shugaban kasar zai kuma kaddamar wa wasu ayyuka da suka hada da rukunin gidajen da Gwamna Babagana Zulum ya gina da wasu tituna a garin Maiduguri.


Sauran su ne Cibiyar Kula da Masu Cutar Kansa a Asibitin Koyarwa na Jami’ar Maiduguri da kuma Tashar Iskar Gas ta kamfanin NNPC.

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki