Search This Blog

Thursday, 2 March 2023

Zamu Kalubalanci Zaben Shugaban Kasa - Atiku Abubakar

Ɗan takarar shugaban ƙasa na babbar jam’iyyar hamayya a Najeriya, PDP, Atiku Abubakar ya ce dole ne kowa ya ƙalubalanci zaɓen da aka yi na ranar 25 ga watan Fabarairu.

A taron manema labarai da ya gabatar a Abuja, tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya ce, abin da ya faru a kan zaɓen fyaɗe ne aka yi wa dumukuradiyya.

Atiku ya ce, a tarihin ƙasar wannan shi ne zaɓe mafi muni da aka taɓa yi, wanda kuma dama ce ta sake daidaita Najeriya.

Amma kuma hukumar zaɓen ƙasar, INEC ta lalata tare da watsa wannan dama da buri na ‘yan Najeriya.

Ɗan takarar na PDP, ya ce zaɓen ya kasa kaiwa matsayi da matakin da aka sa rai zai kai.

Sannan ya ce lauyoyinsu suna duba lamarin kafin su san matakin da za su ɗauka na gaba.

Ya ce idan har ya je kotu ba a yi masa adalci ba to zai bar su da Allah.

Za mu kawo muku karin bayani a nan gaba.
BBC 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Head of Service Urges Civil Servants to Uphold Ethical Conduct

The Head of Service, Kano State, has called on civil servants to strictly adhere to the Civil Service ethical code and show grea...