A taron manema labarai da ya gabatar a Abuja, tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya ce, abin da ya faru a kan zaɓen fyaɗe ne aka yi wa dumukuradiyya.
Atiku ya ce, a tarihin ƙasar wannan shi ne zaɓe mafi muni da aka taɓa yi, wanda kuma dama ce ta sake daidaita Najeriya.
Amma kuma hukumar zaɓen ƙasar, INEC ta lalata tare da watsa wannan dama da buri na ‘yan Najeriya.
Ɗan takarar na PDP, ya ce zaɓen ya kasa kaiwa matsayi da matakin da aka sa rai zai kai.
Sannan ya ce lauyoyinsu suna duba lamarin kafin su san matakin da za su ɗauka na gaba.
Ya ce idan har ya je kotu ba a yi masa adalci ba to zai bar su da Allah.
Za mu kawo muku karin bayani a nan gaba.
BBC