Zamu Kalubalanci Zaben Shugaban Kasa - Atiku Abubakar
ÆŠan takarar shugaban Æ™asa na babbar jam’iyyar hamayya a Najeriya, PDP, Atiku Abubakar ya ce dole ne kowa ya Æ™alubalanci zaÉ“en da aka yi na ranar 25 ga watan Fabarairu.
A taron manema labarai da ya gabatar a Abuja, tsohon mataimakin shugaban ƙasar ya ce, abin da ya faru a kan zaɓen fyaɗe ne aka yi wa dumukuradiyya.
Atiku ya ce, a tarihin ƙasar wannan shi ne zaɓe mafi muni da aka taɓa yi, wanda kuma dama ce ta sake daidaita Najeriya.
Amma kuma hukumar zaÉ“en Æ™asar, INEC ta lalata tare da watsa wannan dama da buri na ‘yan Najeriya.
Ɗan takarar na PDP, ya ce zaɓen ya kasa kaiwa matsayi da matakin da aka sa rai zai kai.
Sannan ya ce lauyoyinsu suna duba lamarin kafin su san matakin da za su É—auka na gaba.
Ya ce idan har ya je kotu ba a yi masa adalci ba to zai bar su da Allah.
Za mu kawo muku karin bayani a nan gaba.
BBC