Hajj 2023: NAHCON, Hukumar Alhazai Na Jihohi Zasu Hada Gwiwa Don Zabar Masauki Masu Inganci

Gabanin bayyana kudin aikin Hajjin shekarar 2023, Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON) ta dorawa Hukumomin Alhazai na Jihohi (SMPB) damar samun matsuguni masu inganci kawai domin rage kudin Hajjin 2023.

NAHCON ta bayyana haka ne a yayin wani taro tsakanin shugabannin hukumomin Alhazai na jahohi da masu samar da masauki da kuma masu aikin hajjin 2023 da aka zabo masu ba da abinci a karo na biyu kafin aikin hajji a ranar Lahadi a birnin Makkah na kasar Saudiyya.

“Eh, kwamishinan kudi na NAHCON wanda ya jagoranci taron ya roke mu da mu nemo masaukai masu inganci da ba shi da nisa da babban masallacin Makkah amma ya kamata a rage farashi.

‘’Farashin masauki a Makkah ya tashi saboda dalilai kamar haka: Masarautar Saudiyya ta fara rusa wasu gidaje da alhazan Najeriya ke amfani da su a baya don share fagen sabon shirinsu na ci gaba.

“Ba kamar a shekarar 2022 da mahajjata miliyan daya kacal suka yi aikin hajji ba, sama da mahajjata miliyan 3 ne ake sa ran za su yi aikin hajji a bana – wanda ke nufin karin yawan mahajjata da karancin masauki. HaÆ™iÆ™a, yana da Æ™alubale a gare mu jahohi amma za mu yi aiki tuÆ™uru don ganin yadda za mu iya tafiya,” wata majiya mai Æ™arfi ta shaida wa manema labarai na Hajji a Makkah.

Binciken da masu aiko da rahotannin alhazai suka yi ya nuna cewa a yanzu haka an ruguje akasarin  otal-otal da ke kan titin Hijra a Misfala yayin da wasu kuma hukumar masarautar Makkah da wuraren tsarki ta Saudiyya ta ruguza su.

Mahajjata daga jihohin Sokoto, Katsina, Kaduna, Bauchi, Kano, Kwara, Plateau da Niger suna karbar maniyyatan su ne a cikin garin Misfala ta hanyar Hijira da Ibrahim Khalil Road a Makkah.

An dage aikin duba masauki da kicin da aka shirya tun karfe 10:30 na rana zuwa karfe 5 na yamma agogon Saudiyya a yau.

Lokaci na duba ya canza saboda yawan zirga-zirga a kewayen Harami musamman bayan sallar tarawihi.
IHR

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki