Hajjin Bana: Hukumar Alhazai Ta Kano Za Ta Ci Da Yin Bita A Wannan Makon Sakamakon Dage Ranar Zabe

Sakamakon dage zabe da hukumar zabe ta kasa ta yi, hukumar Jin dadin alhazai ta Jihar Kano na sanar da Malaman Bita da Kuma Maniyyatan Jihar Kano cewa za'a ci gaba da yin Bitar mako mako a wannan satin wato Asabar da Lahadi 11 da 12 GA watan Maris ,2023 a Cibiyoyin Bita 16 da ke fadin Jihar Kano

Sanarwar wacce Mataimakiyar Daraktar Ilmantarwa da wayar da kan Alhazai ta Hukumar Hadiza Abbas Sanusi ta fitar, ta yi kira ga dukkanin maniyyatan su halarci Cibiyoyin nasu domin akwai fa'ida mai yawa ga yin hakan 

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki