Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Bayyana Gamsuwar Da Yadda Aikin Titin Karkashin Kasa Da Gadar Sama A Tul'udu Da Dan Agundi Ke Gudana

Daga Naziru Idris Ya'u

Gwamnan jihar Kano Injiniya Abba Kabir Yusuf, ya bayyana jin dadinsa kan yadda ake gudanar da ayyukan Tal'udu da DanAgundi na karkashin kasa da gadar sama.

Gwamnan wanda aka gan shi cikin farin ciki a lokacin da ya kai ziyarar bazata inda ya yaba da irin ci gaban da aka samu kawo yanzu.

Gwamna Abba Kabir Yusuf wanda ya samu rakiyar sakataren gwamnatin jihar Dr. Abdullahi Baffa Bichi, Sanatan Kano ta kudu Alhaji Abdulrahman Kawu Sumaila, da ‘yan majalisar zartarwa, ya kai ziyarar duba ayyukan da ake gudanarwa.
Gwamnan ya mika godiyarsa ga ‘yan kwangilar aikin tare da tabbatar wa mazauna yankin cewa gwamnati ta jajirce wajen ganin an kammala wadannan ayyuka a kan lokaci da kuma inganci. Ya kuma kara jaddada cewa abin da gwamnati ta sa a gaba shi ne walwala da ci gaban al’ummar jihar Kano.

Ya samu kyakkyawar tarba daga magoya bayansa da dama wadanda suka daga hannu don nuna godiya da ayyukan da ake gudanarwa. Gagarumin nuna goyon baya na nuni da yadda al'umma suka fahimci alfanun da wadannan gadoji za su kawo bayan kammalawa.
Ana sa ran wadannan gadoji na karkashin kasa da gadar sama za su rage gridlock sosai da inganta aminci da saukin sufuri ga masu ababen hawa a yankin. Gwamna Abba Kabir Yusuf ya lura da muhimmancin wadannan ayyuka wajen inganta rayuwa ga mazauna jihar Kano.


Gwamna Abba Kabir Yusuf shugaba ne nagari mai kishin cigaba da cigaban jihar Kano. Tare da mai da hankali sosai kan ababen inganta rayuwa da jin daɗin jama'a, Gwamna yana ƙoƙarin haɓaka ingancin rayuwa ga duk mazauna. Gwamnatinsa ta himmatu wajen inganta ci gaba mai dorewa da inganta tattalin arzikin jihar baki daya.

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki