Taron majalisar ECOWAS a Kano shine zai kusantar da majalisa ga jama'a-Sanata Barau

 


Baya ga tarukan da suka saba yi a Abuja, Majalisar ECOWAS ta kawo zamanta na ban mamaki na biyu a Kano.


Da yake jawabi ga manema labarai bayan kammala zaman sirri na majalisar ECOWAS, mataimakin shugaban majalisar na farko, Sanata Barau I. Jibrin, ya ce taron zai kara kusantar majalisar da jama’a tare da sanar da su abubuwan da ke faruwa.


Sanata Barau ya ce Kano, kasancewar cibiyar kasuwanci ta  Arewacin Najeriya, ya dace a gudanar da zama na musamman na biyu a Kano.


Sanata Barau ya ce zaman majalisar ECOWAS da za a yi a Kano zai tattauna batutuwan da suka shafi tattalin arziki, tsaro, da sauran al’amuran zamantakewa domin amfanin al’umma baki daya.


A cewar mataimakin shugaban majalisar na farko, majalisar wakilai na kasashe 15 na wannan yanki suna nan Kano, kuma ana son jama’ar Kano su san su, haka kuma majalisar ta san Kano.

(NigerianTracker)

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki