Kotun Koli ta sake tabbatar da Hajiya Laila Buhari a matsayin 'Yar Takarar Sanatan PDP Ta Kano Tsakiya

A ranar Alhamis ne kotun koli ta sake tabbatar da Hajiya Laila Buhari a matsayin ‘yar takarar Sanatan Kano ta tsakiya a jam’iyyar PDP.

SOLACEBASE ta ruwaito cewa a baya kotun daukaka kara ta tabbatar da Laila Buhari ta soke zaben Danburan Nuhu.

Kotun kolin da ta yanke hukuncin da mai shari’a Muhammad Lawal Garba ya karanta, ta yi watsi da dukkan dalilan daukaka kara ta Danburam Nuhu.

Jastis Garba na tare da Jastis Kudirat Kekere Ekun, da Jastis Saulawa da Jastis Ibrahim Jauro, da Jastis Emmanuel Agim

Cikakken labarin zai zo muku nan gaba 

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki