Babu Wanda Nake Tsoro —El-Rufai Ga ‘’Yan Fadar Buhari’

 


Gwamnan Kaduna, Nasir El-Rufai ya kalubalancin ’yan fadar shugaban kasa da yake zargi da zagon kasa ga takarar Bola Tinubu a zaben shugaban kasa da ke tafe. 

Tun a ranar Laraba El-Rufai ya fara tayar da kura da zargin cewa akwai jami’an Fadar Shugaban Kasa da ke neman yi wa takarar Tinubu kafar ungulu.

A wata hirarsa da Sashen BBC na Hausa, an ji shi yana cewa, “Na rantse babu mahalukin da nake tsoro a duk fadin kasar nan.

“Don ana ganin girmn mutum ba soronsa ake ji ba; Amma idan muna girmama mutum, amma yana nuna shi ba babba ba ne, to wallahi za mu ake shi.”

BBC sun fitar da somin-tabin hirar ce kafin a fitar da shi gaba dayansa.

A ranar Laraba, a waya hira da shirin Sunrise Daily na gidan alabijin na Channels ne El-Rufai ya yi zargin akwai magoya baan wadanda suka nemi takarar shugaban kasa a APC wanda Tibubu a lashe da ke fakewa da Shugaba Buhari domin cimma manufofinsu.

A cewarsa, “Suna so mu fadi zabe saboda hakarsu ba ta cim ma ruwa ba; suna da ’yan kararsu , amma an kayar da ’yan kararsu a zaben dan kakara. “Suna so mu fadi zabe, suna fakewa  da shugaban kasa da abin da yake ganin daidai ne,” in ji El-Rufai.

Mai dakin shugaban kasa, Aisha, ta mara wa kalaman na El-Rufai baya, inda ta wallafa bidiyon zargin nasa a shafinta na Instagram.

A zargin na El-Rufai ya i nuni ga wasu da ba mambobin APC ba ne da ke ke fakewa da shugaban kasa wajen cim ma bukaunsu.

Amma Ministan Yada Labarai da Raya Al’adu, Lai Mohammed, ya ce gwamnati ba ta da masaniyar wadanda ke wa Tinubu zagon kasa a Fadar Shugaban Kasa.

A cewarsa, Buhari na daukar daukacin ’yan akra da matsai daya, domin ganin an gudanar da sahihin zabe kuma yana goyon baan Tinubu dari bisa dari.

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki