Hajj2023: Hukumar Alhazai Ta Kano Za Ta Fara Gudanar Da Bitar Alhazai Ga Maniyyata Aikin Hajin bana


Sakataren Hukumar Jin dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Muhammad Abba Danbatta, shi ne ya bayar da wannan umarni ga dukkan Shugabanni da Malaman Bita, na Bitar mako-mako dake fadin jahar Kano 
A sanarwar da Mataimakin Sakataren kwamitin malaman Bitar na Jaha, Malam Dahiru Kabiru Guringawa ya fitar, ta ce akwai shugaban kwamitin Bitar, Sheikh Haroon Muhd Sani Ibn Sina yace, za a fara gudanar da bitar ce daga ranar Asabar 4 ga watan Fabarairu na 2023 da karfe 10 na safe 

Za a fara gudanar da Bitar ce a dukkanin Cibiyoyin bitar dake fadin jahar Kano. 

A saboda sai sanarwar ta yi kira ga dukkanin Jami'an Alhazai na kananan hukumomi dasu tabbata sun sanarwa da dukkanin maniyyatansu don su halarta 

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki