Sakataren Hukumar Jin dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Muhammad Abba Danbatta, shi ne ya bayar da wannan umarni ga dukkan Shugabanni da Malaman Bita, na Bitar mako-mako dake fadin jahar Kano
A sanarwar da Mataimakin Sakataren kwamitin malaman Bitar na Jaha, Malam Dahiru Kabiru Guringawa ya fitar, ta ce akwai shugaban kwamitin Bitar, Sheikh Haroon Muhd Sani Ibn Sina yace, za a fara gudanar da bitar ce daga ranar Asabar 4 ga watan Fabarairu na 2023 da karfe 10 na safe
Za a fara gudanar da Bitar ce a dukkanin Cibiyoyin bitar dake fadin jahar Kano.
A saboda sai sanarwar ta yi kira ga dukkanin Jami'an Alhazai na kananan hukumomi dasu tabbata sun sanarwa da dukkanin maniyyatansu don su halarta