Search This Blog

Thursday, 7 March 2024

Kano-ACReSAL introduces the ESMP and RAP Consultants to Rarin and Bulbula-Gayawa Communities

The State Project Coordinator Dr. Dahir Muhammad Hashim led a team comprising the project staff and the representative of the consultancy firms engaged  for Environment and Social Management Plan (ESMP) and Resettlement Action plan (RAP)studies, to the proposed erosion control sites at Bulbula-Gayawa in Nassarawa and Rarin in Dawakin-Tofa Local Government Areas respectively.

In a Press Release posted on the Facebook page of the outfit, the aim of the visit is to formally introduce them to the communities, to familiarize and to enlighten the communities on the purpose of the engagement and the support expected from them to facilitate successful implementation of the exercise.  

In the quest for royal  blessing for the exercise, the PC appealed to the Sarkin Dawaki Maitutan Bichi   the District Head of Dawakin Tofa, Alhaji Ismail Umar Ganduje, for his continual support towards encouraging communities to adopt the good practices that the ACReSAL project is preaching. 
The Project Coordinator further stated that Kano State Government under the able leadership of his Excellency Engr. Abba Kabir Yusuf is determined to addressing environmental challenges in the state 

In his response, the District Head of Dawakin Tofa, has acknowledges all the efforts and commitment the project has been putting in place to ensure the success of the intervention in the community.
He therefore, called on the community to be good ambassadors, particularly those that are going to be directly  affected by the exercise to ensure that  successful and a hitch free exercise is attained.

Earlier, the Environmental Safeguard Officer Alhaji Mukhtar Bello in his address, spelled out what the consultancies entail as an important instruments in the erosion control work.

The Environment and Social Management Plan (ESMP) and Resettlement Action Plan (RAP) in addition to other instruments are part of the instruments that pave way for mobilization of machinery to project site for construction,  by ensuring that the natural environment is safeguarded, and to also ensure property are judiciously compensated to their rightful owners, he added. 

The team visited the erosion control sites at Bulbula-Gayawa in Nassarawa and Rarin in Dawakin-Tofa LGA.

Participants included SPMU staff under the leadership of the PC, representative of the consultancy firms, traditional councils, Site Committee, Community Association members of the community among others

Wednesday, 6 March 2024

Gwamnatin Kebbi Za Ta Raba Man Fetur Kyauta Ga Manoma

Gwamnatin Kebbi ta bullo da shiri na musamman domin raba man fetur kyauta ga manoman rani da nufin saukaka musu yin wahalar noma a jihar.

Kwamishinan Noma na jihar, Shehu Mu’azu ya ce gwamnatin ta samar da haujin noma, inda aka farrfado da aikin noma domin jihar ta cigaba da rike kambunta a bangaren noman shinkafa a Nijeriya.


Saboda haka ne ta gina karamin wurin noma na zamani a kananan hukumomin Argungu da Fakai a garin Mahuta.

Wannnan a cewarsa, kari ne a kan tallafin noman rani da manoman shinkafa 30,000 da masu noma masara 7,500 da kuma masu noman rogo 2,000 suka samu daga gwamnatin.
(AMINIYA)


Tuesday, 5 March 2024

Matukin Adaidaita Sahu Dan Kano Da Ya Tsinci Kudi Ya Mayar, Ya Samu Tallafin Miliyan 250 Don Yin Karatu

A wani abin da ya yi kama da gasa, matashin nan mai tuka Adaidaita Sahu mai shekaru 23 a Kano, Auwalu Salisu, wanda ya tsinci kudin wani dan kasuwa dan kasar Chadi har naira Miliyan 15  da ya manta su a kekensa tun a 2023, an ba shi tallafin karatu na naira Miliyan 250 har zuwa matakin karatun digiri na uku 

KANO FOCUS ta ruwaito cewa, LEADERSHIP Media Group ta yi bikin karamar  Auwalu a ranar Talata a wajen taron shekara-shekara da kuma bikin karramawa a matsayin wanda ya lashe lambar yabo ta ‘Fitaccen matashin matashin shekarar 2023’, saboda nuna gaskiya da ya yi.

Dan takarar shugaban kasa a jam’iyyar Labour Party (LP), Peter Obi, wanda aka karrama shi a matsayin Gwarzon dan siyasar LEADERSHIP na shekarar 2023, shi ne ya fara ba Awwalu guraben karatu a Jami’ar Baze da ke Abuja har zuwa matakin digirin digirgir.


Bayan haka, gwamnan jihar Neja, kuma wanda ya lashe kyautar Gwarzon Gwamnan na LEADERSHIP, Mohammed Umar Bago, ya mayar da martani cikin raha yana mai cewa jam’iyyar Labour ba za ta iya zarce jam’iyyar APC mai mulki ba.

A sakamakon haka Bago ya sanar da kyautar N250m ga Awwalu don jin dadin aikinsa na gaskiya da kuma karfafawa sauran matasan Najeriya kwarin gwiwa don nuna halin kirki.

Ya ce Awwalu zai samu tallafin Naira miliyan 50 kowanne daga gare shi da kansa da kuma shugaban kasa Bola Tinubu da ministocinsa da kungiyar gwamnonin APC da kuma gwamnatin jihar Neja.


Bago ya kara da cewa zai bayyana daya daga cikin ayyukan tituna da yake gudanarwa a jihar Neja da sunan matukin babur din na Kano.

Saturday, 2 March 2024

Use of Micro-Nutrients a vital step for curbing maternal mortality rates - Sunday Okhoronko

Mr Sunday Okworonko,the Executive Secretary of Civil Society Organization, CS-SUNN ;that tackles malnutrition issues gave the advice during a 2 day media capacity training held  in Abuja .

Speaking while declaring the workshop open, the Executive Secretary said the training became  imperative with regard to the need to put effort together in ensuring the reduction of aneamia through the use of Multiple Micronutrients in Nigeria.

Mr Sunday  Okoronkwo stated that there is need for the quick response from the government to tackle the challenges of the prgnant women faces  saying that aneamia and hunger are the major problems that affects millions, particularly women and adolescent girls across the country. 

 He explained that media professionals have a  vital role  to play in advocasing for the government and stakeholders to fight for the Anaemia in pregnant women , adolescents and malnutrition in children as it causes the loss of million  of lives adding that dietary diversity and use of essential micro nutrients  supplements, MMS will prevent the menace.

Speaking while presenting a paper, titled' Nigeria’s Nutrition Situation with focus on Micronutrients Deficiencies and Anaemia Prevalence in Nigeria', the Head of Food and Nutrition Division , Federal Ministry of Budget and National Planning, Mrs Chito Nelson said statistics showed  that 149 million Children under the age of five are stunted globally ,which lead to 50% dealth of Children under 5.

She maintained that when  child is malnourished his  chances of  dying are high adding that 45 million Children under the age of 5 are wested across the world,97% of these children are in Asia (31.6 million) and Africa (12.2 million).

Mrs Nelson noted  that to achieve the stated objectives, there is  the need for coordinated platform and media advocacy on policy makers with the aim of ensuring effective policy making and good political will.

Friday, 1 March 2024

CBN Ya Soke Lasisin ’Yan Canji 4,173 A Faɗin Nijeriya

Babban Bankin Najeriya (CBN) ya sanar da soke lasisin gudanar da ayyuka na wasu ’yan canji 4,173 a faɗin ƙasar nan take.

CBN ya ce daga cikin ’yan canjin da soke lasisin ya shafa akwai waɗanda suka gaza sabunta lasisinsu, da waɗanda suka gaza biyan wasu caje-caje kuɗin gudanarwa da Babban Bankin ya rataya a wuyansu.


Haka kuma, daga cikin waɗanda abin ya shafa akwai masu bijire wa dokokin Babban Bankin kan tsare-tsarensa na yaƙi da safarar kuɗaɗen haram, dakile fitar da kuɗaɗen da ke ɗaukar nauyin ayyukan ta’addanci, da kuma dakile ka’idojin samar da kuɗaɗe.

Kazalika, CBN ya ce waɗanda aka soke wa lasisin akwai masu rashin mika wa CBN ɗin bayanan yadda suke sayar da dalar duk mako.


Wannan matakin wani ɓangare ne na ƙoƙarin da CBN da Gwamnatin Tarayya ke yi na maido da ƙwarin gwiwa a kasuwar canji da musayar kuɗaɗen waje da kuma farfaɗo da tattalin arzikin ƙasar.

CBN dai ya yi alƙawarin ci gaba da bayar da dala ga masu kamfanin canjin kuɗin a kowanne mako kamar yadda aka saba a baya.

Sai dai ya kuma lashi takobin hukunta duk wanda ya saɓa ƙa’idar da aka shimfida ta gudanar da hada-hadar a Najeriya.

(AMINIYA)

Thursday, 29 February 2024

'Yan Bindiga Sun Sace Mutum Talatin Lokacin Sallah A Zamfara

Wani ganau ya ce ’yan bindigar sun mamaye masallacin ne da misalin karfe 5 na Asuba, a lokacin da ake shirin fara salla.

Garba ya ce, “Za mu fara sallar asuba, kwatsam sai ’yan bindiga suka shigo masallaci suka umarci kowa ya fito ya bi su.

“Kowa ya yi kokarin guduwa domin tsira amma suka tare ko’ina suka gargade mu cewa za su kashe duk wanda ya yi yunkurin guduwa.


“Na samu na iya tsalle daga tagar kuma da sauri na shiga wani kango da ke kusa da masallacin na boye kaina,” in ji shi.
Shaidan ya bayyana cewa ’yan bindigar sun bar baburansu a nesa da masallacin don kada a lura da motsinsu.

Ya kara da cewa, “Daga baya sun tafi da mutanen zuwa inda baburansu suke, suka tafi da su.”

A cewarsa, adadin mutanen da aka sace a masallacin zai iya wuce 30.

Ya kara da cewa “masallacin ya cika a lokacin da suka kai hari kuma kadan ne daga cikin mu suka samu tsira.”

Daya daga cikin shugabannin yankin wanda ya nemi a sakaya sunansa ya ce jami’an tsaro na ci gaba da bin diddigin ’yan bindigar domin kubutar da wadanda aka sacen.


Karamar hukumar Tsafe dai na daga cikin kananan hukumomin jihar da ke fama da matsalar ’yan bindiga.

Titin Tsafe zuwa Gusau ya zama wuri mafi hadari a jihar inda a kullum ake sace mutane.

A ’yan kwanakin nan an kashe ’yan bindiga da dama a karamar hukumar lokacin da wasu gungun ’yan bindiga guda biyu suka yi arangama.

(AMINIYA)

Wednesday, 28 February 2024

Sababbin Shugabannin NAHCON Sun Kama Aikinsu Bayan Da Mataimakin Shugaban Kasa Ya Kaddamar Da Su

A ranar Laraba ne Hukumar kula da aikin Haji ta kasa ta shaida wani muhimmin lamari, yayin da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya kaddamar da shugabancinta a karo na biyar karkashin jagorancin Malam Jalal Ahmed Arabi Taron kaddamarwar ya faru ne a ofishin mataimakin shugaban kasar, inda bayan nan ne shugabannin suka zarce zuwa hukumar

A sanarwar da mataimakiyar daraktar harkokin hulda da jama'a da dab'i ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, tace a yayin gudanar da taro shugabannin hukumar ta NAHCON, shugaban hukumar, Malam Jalal Arabi, yayi maraba da dukkanin wakilaninda ya bayyana kwarin gwiwarsa ga cancantarsu, inda ya kuma basu tabbacin samun hakan daga bangaren ma'aikatan hukumar kamar yadda shi ma ya samu yayin da ya kama aiki a watanni hudun da suka gabata.
Daga nan sai yayi kira ga ma'aikatan hukumar su bayar da makamancin hadin kan sababbin shugabannin nasu don cimma manufar hukumar

Sababbin shugabannin da aka nada sun hada da

1. Malam Jalal Ahmed Arabi Shugaba

2. Aliu Abdulrazaq - Kwamishinan Kudi da harkokin ma'aikata

3. Prince Anofi Elegushi - Kwamishinan ayyukan Haji

4. Farfesa Abubakar A Yagawal - Kwamishinan bincike da tsare-tsare

Wakilan Shiyya

1. Dr Muhammad Umaru Ndagi - Dan hukumar gudanarwa Mai wakiltar Arewa ta tsakiya

2. Abba Jato Kala - Mai wakiltar Arewa ta gabas

3. Sheikh Muhammad Bin Uthman - Mai Wakiltar Arewa ta yamma

4. Tajudeen Oladejo Abefe - Mai wakiltar Kudu maso yamma

5. Aishat Obi Ahmed - Mai wakiltar Kudu maso Gabas

6. Zainab Musa - Mai wakiltar Kudu maso kudu

7. Farfesa Musa Inuwa Fodio - Wakilin Jama'atul Nasrul

Islam

8. Farfesa Mahfouz Adebola - Mai wakiltar majalisar koli ta harkokin addinin musulunci

Bayan nuna godiyarsu, sababbin shugabannin sun kumabyaba da rawar da shugaban ya taka

A jawabansu daban-daban yayin taron, sun bayar da tabbacin goyawa shugaban hukumar ta NAHCON baya don samun nasara
Sun kuma nuna godiyarsu ga Allah bisa damar da ya basu su yi wannan hidima tare da yin addu'ar samun jagora daga Allah don sauke nauyin da ya rataya a kansu A jawabinsa y rufe taron,

Mataimakin Shugaban Kasa Ya Kaddamar Da Sababbin Shugabannin NAHCON

Mataimakin shugaban kasa, Sanata Kashim Shettima ya kaddamar da sababbin Jami'an hukumar alhazai ta kasa (NAHCON) tare da yin kira ga da su bullo da sabbin abubuwa a harkokin aikin hajji a Najeriya. 

A sanarwar da mai taimakawa Mataimakin Shugaban kasar kan harkokin yada labarai Stanley Nkwocha ya sanyawa hannu, yace da yake jawabi yayin kaddamar da sababbin 'yan hukumar a fadar shugaban kasa da ke Abuja ranar Laraba, mataimakin shugaban kasar ya bukaci mambobin su hada kai tare da kawo sabbin ra’ayoyi kan ayyukan hukumar. A cewar Sanata Shettima, yin aiki a hukumar NAHCON na da matukar muhimmanci ganin cewa “Hajji na daya daga cikin rukunan Musulunci guda biyar”. “A gare ku, bayan nadaku da aka yi, abu ne mai nasara domin idan kun yi wa alhazai hidima da kyau, Allah Ta’ala zai biya ku a ranar lahira. Don haka, aikinku ya fi kusanci da na addini fiye da aikin gudanarwa,” in ji Shettima. 
Da yake karin haske game da batun kafa sabuwar hukumar da aikin da ke gabansu, Sanata Shettima ya ce, “Shugaban yana sane ya zabo mutanen da ke da al’adu daban-daban da kuma wadanda ba a taba gurbata su a baya ba domin su kawo sabbin dabaru da sabbin abubuwa a harkokin aikin Hajji a Najeriya da kuma yadda za a yi aikin Hajji a Najeriya. haka kuma a yi tambayoyi game da tsarin gudanarwa na hukumar tare da fitar da mafi kyawu daga ma'aikatan." “Kamar yadda aka saba, za ku fuskanci kalubale da dama amma ina rokon ku da ku hada karfi da karfe guda domin cimma nasarar da muke bukata. 

Zan roke ku da kuyi tunani ku fito da ingantattun hanyoyin da za su gamsar da alhazan Najeriya. “Aiki ne mai wuyar gaske; wannan shi ne yanayin aikin hajji. Amma ina so ku kasance da shi a cikin zuciyarku cewa kuna bauta wa Allah da bil'adama," in ji shi. Mataimakin shugaban kasan ya bukaci sabbin jami’an da su inganta tsarin adashin gata mai dogon zango na aikin Hajji domin kara yawan maniyyatan da ke halartar ibadar ta shekara a fadin kasar nan. Yace: "Akwai Jihohin da suka samu nasara a cikin shirin adashin gata mai dogon zango na Ja'iz, kuma akwai bukatar a kara ba da shawarwari ta yadda wannan tsari ya kasance anyi koyi da shi a fadin kasar nan." 
Ya kuma kalubalanci hukumar da ta “hadi da jami’an mu da abokan huldar mu don samar da dangantaka mai dorewa ta yadda za su samu jarin jari mai yawa a ayyuka a kasa mai tsarki.” 

Tun da farko a nasa jawabin shugaban Hukumar kula da aikin Haji ta kasa,  Malam Jalal Arabi ya godewa shugaban kasa da mataimakinsa bisa ganin sun cancanci yiwa kasa hidima ta hanyar hukumar NAHCON. 
Ya ce bisa la’akari da muhimmancin aikin da ke gabansu, sabuwar hukumar za ta yi aiki a matsayin tawaga don inganta ayyukan Hajji a Najeriya, tare da bayar da tabbacin cewa maniyyatan za su samu darajar kudinsu. 

Shugaban hukumar ta NAHCON ya ce tuni tawagar sa ta fara aiki da ziyarar da ta kai kasar Saudiyya domin duba wuraren da za a fara gudanar da ayyuka a nan gaba. 

Sabon shugabancin hukumar da aka kafa ya hada da Aliu Abdulrazaq (Kwamishinan harkokin Ma'aikata da kudi), Prince Anofi Elegushi (Kwamishina, Ayyukan Haji), da Farfesa Abubakar A. Yagawal (Kwamishina, Tsare-tsare & Bincike). Wakilan shiyyar da masu ruwa da tsaki sun hada da Dr. Muhammad Umaru Ndagi — Arewa ta tsakiya; Abba Jato Kala - Arewa maso Gabas; Sheikh Muhammad Bin Othman - Arewa maso Yamma; Tajudeen Oladejo Abefe - Kudu maso Yamma; Aishat Obi Ahmed - Kudu maso Gabas; Zainab Musa - Kudu maso Kudu; Farfesa Musa Inuwa Fodio — Jama’atul Nasril Islam, da Farfesa AdedimiziMahfouz Adebola - Majalisar Koli kan Harkokin Musulunci. 
Har ila yau, wadanda suka halarci taron sun hada da ministan lafiya da walwalar jama’a, Farfesa Muhammad Ali Pate; Ministocin sufurin jiragen sama, Mista Festus Keyamo, SAN, da na cikin gida, Mista Olubunmi Tunji-Ojo. 

Monday, 26 February 2024

Jinkirin Mika Fasfon Maniyyata Na Kawo Cikas Ga Aikin Yin Bizar Aikin Hajji - Laminu Rabi'u

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa, ya bayyana jinkirin mika fasfo  ga hukumar a matsayin babban kalubalen da ke kawo cikas wajen yin Bizar aikin Hajji ga maniyyata

Yayin wata ziyara zuwa daya daga cikin cibiyoyin bitar Alhazai  da aka gudanar a karamar hukumar Doguwa a yau, Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa ya jaddada muhimmancin bayar da fasfo a kan lokaci wajen saukaka gudanar da bizar aikin Hajji cikin sauki ga maniyyata.

A cikin sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Sulaiman Abdullahi Dederi ya sanyawa hannu, yace Alhaji Danbappa, wanda wakilin hukumar gudanarwa na hukumar, Malam Ismail Mangu ya wakilta, ya bayyana cewa, “jinkirin tura fasfo na kasa da kasa yana kawo cikas wajen gudanar da aikin Hajji yadda ya kamata ga maniyyatan mu, ya zama wajibi mu daidaita wannan aiki domin tabbatar da kammala aikin a kan lokaci. da kuma inganta aikin hajji gaba daya”.

Malam Ismail Mangu ya kara jaddada muhimmancin hada hannu da hukumar kula da shige da fice ta Najeriya da kuma bin ka’idojin da masu ruwa da tsaki a harkar bayar da fasfo da biza suke da shi domin rage jinkiri da kuma tabbatar da tafiya mara inganci ga maniyyatan da suke gudanar da aikin Hajji mai alfarma.

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, ta jajirce wajen ganin ta magance kalubalen da kuma inganta yadda ake gudanar da aikin hajji, tare da jaddada sadaukarwarta na samar da ayyuka na musamman ga alhazai.

Yankunan da aka ziyarta sun hada da kananan hukumomin Doguwa da Tudun-wada.




Sunday, 25 February 2024

Babu hannunmu a tashin farashin kayan abinci -- Dangote

Babbar Darakta a rukunin kamfanonin Dangote, Hajiya Fatima Aliko Dangote, ta bayyana cewa rukunin kamfanonin Dangote ba su da hannu a tashin farashin kayayyakin abinci da ake fuskanta a kasar nan.

Daily Nigeria Hausa ta rawaito cewa wata hira da Sashen Hausa na BBC, Hajiya Fatima ta ce kamfanin ya sayar da bangaren sarrafa abinci shekaru biyar da suka gabata ga Olam Group da ke sarrafa abinci da kasuwancin noma a Najeriya.

Ta ce Olam a yanzu shi ne ke samar da fulawa, taliya, semolina, kuma duk wata fulawa da ake samu a kasuwanni ba kamfanin Dangote ne ke samar da ita ba.

“A cikin yarjejeniyar cinikin, an amince da cewa za su ci gaba da yin amfani da sunanmu da tambarin muwajen yin kayayyakinsu, kuma nan da shekara mai zuwa za su daina.

“Mu yanzu sukari, gishiri, da kayan yaji na Dangote kawai muke samarwa. Har ila yau, muna fatan za mu fara noman shinkafa nan gaba ko kuma badi,” in ji ta.

Fatima ta kara da cewa ba su ji dadin yadda farashin kayayyakin ke hawa ba kuma kamfanin ba zai iya maganin hakan ba, inda ta nuna fatan abubuwa za su daidaita nan ba da jimawa ba.

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

IHRC-RFT Nigeria Expresses Concern Over the Increasing Cross-Border Movement of Pastoralists and Their Livestock

The International Human Rights Commission – Relief Fund Trust (IHRC-RFT) Nigeria Chapter, an organization with Special Consultat...