Sababbin Shugabannin NAHCON Sun Kama Aikinsu Bayan Da Mataimakin Shugaban Kasa Ya Kaddamar Da Su

A ranar Laraba ne Hukumar kula da aikin Haji ta kasa ta shaida wani muhimmin lamari, yayin da mataimakin shugaban kasa Kashim Shettima ya kaddamar da shugabancinta a karo na biyar karkashin jagorancin Malam Jalal Ahmed Arabi Taron kaddamarwar ya faru ne a ofishin mataimakin shugaban kasar, inda bayan nan ne shugabannin suka zarce zuwa hukumar

A sanarwar da mataimakiyar daraktar harkokin hulda da jama'a da dab'i ta hukumar, Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, tace a yayin gudanar da taro shugabannin hukumar ta NAHCON, shugaban hukumar, Malam Jalal Arabi, yayi maraba da dukkanin wakilaninda ya bayyana kwarin gwiwarsa ga cancantarsu, inda ya kuma basu tabbacin samun hakan daga bangaren ma'aikatan hukumar kamar yadda shi ma ya samu yayin da ya kama aiki a watanni hudun da suka gabata.
Daga nan sai yayi kira ga ma'aikatan hukumar su bayar da makamancin hadin kan sababbin shugabannin nasu don cimma manufar hukumar

Sababbin shugabannin da aka nada sun hada da

1. Malam Jalal Ahmed Arabi Shugaba

2. Aliu Abdulrazaq - Kwamishinan Kudi da harkokin ma'aikata

3. Prince Anofi Elegushi - Kwamishinan ayyukan Haji

4. Farfesa Abubakar A Yagawal - Kwamishinan bincike da tsare-tsare

Wakilan Shiyya

1. Dr Muhammad Umaru Ndagi - Dan hukumar gudanarwa Mai wakiltar Arewa ta tsakiya

2. Abba Jato Kala - Mai wakiltar Arewa ta gabas

3. Sheikh Muhammad Bin Uthman - Mai Wakiltar Arewa ta yamma

4. Tajudeen Oladejo Abefe - Mai wakiltar Kudu maso yamma

5. Aishat Obi Ahmed - Mai wakiltar Kudu maso Gabas

6. Zainab Musa - Mai wakiltar Kudu maso kudu

7. Farfesa Musa Inuwa Fodio - Wakilin Jama'atul Nasrul

Islam

8. Farfesa Mahfouz Adebola - Mai wakiltar majalisar koli ta harkokin addinin musulunci

Bayan nuna godiyarsu, sababbin shugabannin sun kumabyaba da rawar da shugaban ya taka

A jawabansu daban-daban yayin taron, sun bayar da tabbacin goyawa shugaban hukumar ta NAHCON baya don samun nasara
Sun kuma nuna godiyarsu ga Allah bisa damar da ya basu su yi wannan hidima tare da yin addu'ar samun jagora daga Allah don sauke nauyin da ya rataya a kansu A jawabinsa y rufe taron,

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki