Gwamnatin Kebbi Za Ta Raba Man Fetur Kyauta Ga Manoma

Gwamnatin Kebbi ta bullo da shiri na musamman domin raba man fetur kyauta ga manoman rani da nufin saukaka musu yin wahalar noma a jihar.

Kwamishinan Noma na jihar, Shehu Mu’azu ya ce gwamnatin ta samar da haujin noma, inda aka farrfado da aikin noma domin jihar ta cigaba da rike kambunta a bangaren noman shinkafa a Nijeriya.


Saboda haka ne ta gina karamin wurin noma na zamani a kananan hukumomin Argungu da Fakai a garin Mahuta.

Wannnan a cewarsa, kari ne a kan tallafin noman rani da manoman shinkafa 30,000 da masu noma masara 7,500 da kuma masu noman rogo 2,000 suka samu daga gwamnatin.
(AMINIYA)


Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki