Jinkirin Mika Fasfon Maniyyata Na Kawo Cikas Ga Aikin Yin Bizar Aikin Hajji - Laminu Rabi'u

Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa, ya bayyana jinkirin mika fasfo  ga hukumar a matsayin babban kalubalen da ke kawo cikas wajen yin Bizar aikin Hajji ga maniyyata

Yayin wata ziyara zuwa daya daga cikin cibiyoyin bitar Alhazai  da aka gudanar a karamar hukumar Doguwa a yau, Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa ya jaddada muhimmancin bayar da fasfo a kan lokaci wajen saukaka gudanar da bizar aikin Hajji cikin sauki ga maniyyata.

A cikin sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Sulaiman Abdullahi Dederi ya sanyawa hannu, yace Alhaji Danbappa, wanda wakilin hukumar gudanarwa na hukumar, Malam Ismail Mangu ya wakilta, ya bayyana cewa, “jinkirin tura fasfo na kasa da kasa yana kawo cikas wajen gudanar da aikin Hajji yadda ya kamata ga maniyyatan mu, ya zama wajibi mu daidaita wannan aiki domin tabbatar da kammala aikin a kan lokaci. da kuma inganta aikin hajji gaba daya”.

Malam Ismail Mangu ya kara jaddada muhimmancin hada hannu da hukumar kula da shige da fice ta Najeriya da kuma bin ka’idojin da masu ruwa da tsaki a harkar bayar da fasfo da biza suke da shi domin rage jinkiri da kuma tabbatar da tafiya mara inganci ga maniyyatan da suke gudanar da aikin Hajji mai alfarma.

Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, ta jajirce wajen ganin ta magance kalubalen da kuma inganta yadda ake gudanar da aikin hajji, tare da jaddada sadaukarwarta na samar da ayyuka na musamman ga alhazai.

Yankunan da aka ziyarta sun hada da kananan hukumomin Doguwa da Tudun-wada.




Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki