Search This Blog

Tuesday, 9 May 2023

Abun Da Ya Haddasa Yakin Sudan Jamhuriyar Musulunci (Kashi na daya) - Datti Assalafiy

Datti Assalafiy✍️

Shimfida:
Akwai taba addini a yakin Sudan, saboda shi tsohon shugaban Kasar Sudan Umar Albashir wanda aka masa tawaye aka hambarar dashi da karfin tsiya ya bawa Musulunci kariya sosai a Sudan, yana bawa Musulunci kariya a Sudan wanda ko Saudiyyah bata yin irinsa a Kasarta

Yana daya daga cikin shugabannin Kasashen Musulunci a duniya wanda idan makiya Musulunci suka taba addinin Allah da Musulmai yake fitowa yayi magana, Kasar Iran daular masu bin addinin shi'ah sun taba yin mummunan batanci ga Sahabban Annabi (SAW) guda biyu Abubakar da Umar, a ranar ya kori Ambasadar Kasar Iran, kuma yasa aka rushe embassy na Iran dake Sudan, aka gina Sabon Masallaci a gurin, aka sanya wa Masallacin sunan Abubakar da Umar wato sunan Sahabban Annabi (SAW)

Lokacin Shugaba Umar Albashir babu gidan sayar da giya a Sudan, babu gidan karuwai a Sudan, babu gidan caca da sauran guraren sabon Allah, mata basa shiga harkokin shugabanci, to wannan kariyar da ya bawa Musulunci, sai Kasar Amerika ta dauki hayar wasu gurbatattun Musulmai suka tayar da zanga-zanga mai taken "HURRIYA-SALAMA-ADALA". ma'ana 'yanci, adalci da zaman lafiya, wato su sun gaji da dokokin Musulunci tsaurara suna neman 'yanci don suyi rayuwa irin na yahudu da nasara, akan haka suka kifar dashi, to Allah suka taba

A lokacin da suke dab da zasu kifar da Albashir, ya fito yayi rantsuwa yace Billahillazi zaku ce na fada muku idan kuka sake kuka hada kai da Amerika, Wallahi sai kunyi da na sanin abinda kuke min na zanga-zanga da tawaye, to bayan sun kifar dashi, shugaban Sojojin Sudan General Abdel Fattah al-Burhan da ya maye gurbinsa karen farautar Amerika da Isra'ila ne, nan take ya bude wa Kasar Isra'ila hanyar mubayi'ah, kuma kafin fara wannan yakin, a ranar 1-2-2023 General Al-Burhan ya gayyato Ministan harkokin waje na Kasar Isra'ila Eli Cohen zuwa Khartoum babban birnin Sudan, wannan ne abinda ya faranta ran Amerika ta cire manyan takunkumi da ta kakabawa Sudan lokacin mulkin Umar Albashir, kuma ta nemi Shugaban Sojojin ya mika mata Albashir don ta wulakantashi

An yaudari Mutanen Sudan da neman 'yanci, to ga inda 'yancin ya kaisu a yau, mutum sama da dubu dari uku suna sansanin 'yan gudun hijra a sati uku da aka fara wannan yakin, 'yan Sudan sama da dubu dari da hamsin sun tsere daga Kasar, an kashe mutane kusan dubu daya zuwa yanzu, asibitoci sun rufe, manyan kasuwanni sun rufe, babu inda za'a kai marassa lafiya, kafar internet na Kasar na neman rufewa gaba daya, harkokin bankuna na Kasar duk sun tsaya saboda mummunan harin bomb da akayi a babban bankin Kasar Sudan, farashin kudin Sudan yayi mummunan karyewa mafi muni a tarihi, a tsakanin sati uku da fara wannan yakin anyi barna a Sudan wanda za'a dauki tsawon lokaci kafin a gyara lamura, na karanta bayanin wani masanin tsaro yace za'a kai nan da shekaru 15 kafin Sudan ta dawo hayyacinta ko a gama wannan yakin

Wannan bayanin da nayi shinfidane kawai, ku biyoni a rubutu na gaba don jin abinda ya haddasa wannan yaki da tarihin yakin, da inda aka nufa, akwai babban darasi garemu akan wannan kazamin yaki da yake faruwa a Sudan
 
Muna rokon Allah Ya tausaya wa bayinSa salihai da kananan yara da mata dake Sudan Ya kawo musu mafita na alheri

Allah Ya sa fitinar ta cinye wadanda suka tayar da ita da wadanda suka tsara zanga-zangar kifar da shugaba Umar Albashir 


Game Da Tafiya A Motar Haya Kashi Na 3 - Dr Dukawa


HALIN DA WASU TASHOSHIN MOTA SUKE CIKI 

A bisa kiyasi, tashar Na’ibawa a Kano ba za ta gaza shekara arba’in (40) ba. Saboda an samar da ita ne a zamanin marigayi gwamnan tsohuwar jihar Kano Alhaji Abubakar Rimi (1979 – 1983). Amman har izuwa yau tashar tananan jiya ya yau: kango wanda babu wani abu da yake nuna ana samun kudi a wurin; babu kwalta, babu interlocks, babu dabe kowane iri! Zaiyar kasa. Sai yalwar leda da sauran nau’i na shara. Babu wani lafiyayyen makewayi. Da na bukaci wurin yin bawali sai aka nuna min wani uban juji a yammacin cikin tashar. Sai da roki wani dan bola jari cewar ya dan kauce zan kama ruwa. 

Na tabbatar idan ruwa ya sauka mummunan halin da tashar ke ciki ba zai gaza na tashar Unguwa Uku ta Kano ba, wacce na yi rubutu akan nata halin da take ciki a sherarar 2020. 

An yayyanka pilotai a cikin tashar Na’ibawa. Wasu an gina shaguna ana gudanar da ciniki wasu kuma an saka fandisho na gini ba a yi ginin ba. Babu Masallaci sai ‘yar musalla amman har da lasifika. Ko yaya aka yi a kasar Musulmi irin Kano za a yi tashar mota ta shekara arba’in ba a samar da masallaci ba sai abin ya daurewa mutum kai. Alhali ya kamata ace izuwa yanzu har dakin shan magani, da karamin dakin ATM da ofishin aika sako (akwatin gidan waya) na gaggawa, da kuma ofishin ‘yansanda ya kamata ace an samu.

Halin da na samu tashar mota a Yola da Jalingo bai sha banban da yadda na baro a Kano ba. Babu wani abu na cigaba. Sai turbaya da shara da bola.
Anan zan nanata kirana ga kananan hukumomi (LGAs) a Arewacin Najeriya cewar su tuna amanar da suka dauka na gudanar da ayyukan da aka zayyana a makale na hudu (fourth schedule) na Tsarin Mulkin Najajeriya. Daga ayyukansu akwai samarwa da kula da tashoshin mota. Wannan ba ya nufin a shata kango motoci su rika shiga suna lodi ‘yan rabanu (masu karbar kudin shiga) kuma suna karbar haraji kawai ba. 

Amman yana nufin a inganta tashoshi ta hanyar samar da yanayi mai kyau da tsabta da tsaro. Kunyoyin da suke karbar nasu kason a wurin direbobi su ma su sani cewar babban aikinsu shine su inganta sana’ar ta hanyar bibiyar hukumomi da neman su sauke nauyinsu da kuma taya hukumomin samar da wasu abubuwan inganta rayuwa a wurin sana’a. sabanin haka za su rika cin haram ne na wannan kudaden da suke karba.

Monday, 8 May 2023

'Yan sandan Najeriya sun ceto mutane 58 daga hannun 'yan bindiga

 


‘Yan sanda a Najeriya sun ce sun ceto mutane 58 da ‘yan ta’adda suka yi garkuwa da su a jihar Kogi, yayin da daya daga cikin wadanda aka yi garkuwa da sun ya rasa ransa yayin artabu tsakanin jami’an tsaro da ‘yan ta’addan

A cikin wata sanarwa da kakakin rundinar ‘yan sandan jihar Josephine Adeh ta fitar a wannan Lahadin, ta ce wannan nasara da suka samu wani bangare ne na aikin hadin gwiwa tsakanin rundunar da sauran jami’an tsaro, tare da hadin gwiwar ‘yan banga da mafarautan jihar. 

Adeh ta ce lamarin ya faru ne a dajin Udulu da ke Karamar Hukumar Gegu mai nisan kilomita 145 daga bababban birnin tarayya kasar. 

A cewarta, an yi musayar wuta tsakanin ‘yan ta’addan da kuma jami’an tsaro kuma daga bisani suka tsere suka bar mutanen da suka yi garkuwa da su.  

Sai dai bata bayyana inda aka sace mutanen ba da kuma tsawon lokacin da suka dauka a hannun ‘yan ta’addan.  

RFI

Game Da Tafiya A Motar Haya Kashi Na Biyu


 


Daga Dr Sa'idu Ahmad Dukawa

TSARIN DAUKAR FASINJA A TASHA

Bayan da na yi tambayi game da tsarin daukar fasinja a tashar mota, na sami bayanin cewa mutum zai iya zuwa tsahar Na’ibawa (wacce a yanzu aka sakawa suna “tashar Kano Line”) ya yi booking (biyan kudi kafin ranar tafiya). Don haka sai na je ofishin Adamawa Sunshine (wanda alal hakika shago ne a cikin tashar da dan teburi da mutumin da yake karbar kudi ya rubuta rasiti), na biya kudina ana kashegarin ranar tafiya.

Na tambaya mutum nawa ake dauka a mota kirar sienna? Aka ce min ana daukar mutum takwas ne, fasinja biyu a gaba, uku a tsakiya, uku a karshe. Amman fa Bature ya yi motar ne domin daukar fasinja biyar: guda a gaba, biyu a tsakiya, biyu a karshe. Don haka ana wuce kima (overload) na mutum uku. A motar ‘yankasuwa kuwa har mutum hudu ake sakawa a tsakiya, kamar yadda na ganewa idona a yayin dawowata daga Jalingo zuwa Kano. Allah ya kiyaye, a duk lokacin da aka gamu da hadari, za ta yiwu a yi asarar rayuka tara zuwa goma a cikin mota guda. A inda aka san kimar rai, duk yadda za a yi a rage asarar rai guda ana yi.

Ko me yasa dole sai an yi overload a motocin haya a Najeriya? Dalilan sanannu ne. farko dai akwai tsadar man fetur. Na biyu akwai biyan haraji hawan hawa, hukuma ta karba, kungiyoyi su amsa, yan kamasho su yaga, a dankawa ‘yan wururu masu taro fasinja daga hanya su kawo shi gindin mota, a dankawa masu gadin tasha, a yi ta mikawa jami’an tsaro kashi kashi (na kidaya shingen jami’an tsaro kimanin dozen guda a tsaknin Jalingo da Gombe kadai). Ga kuma tsadar kayan mota (spare parts) tunda kusan komai sai an yi odarshi, ba a kera komai a kasar. Ga mamallakin mota yana so ya mayar da kudinsa da wuri, don haka yana son a rika kawo balance mai tsoka a duk rana.

A karshe ga bukatar Direban motar na ya samu abinda zai shiga gida da shi ya sallami iyali. Idan aka hada duk wadannan bukatun akan fasinja kuma ba zai iya dauka ba. Don haka akan dole ake gwammacewa a cunkusa fasinja, wani a jikin wani, kamar kifin sardine.

Akwai kuma abinda yake ya shafi dabi’a ta rashin tsari da ci da zuci da rashin ganin kimar dan Adam wacce take tattare da mutane da yawa, barin idan sun san babu wata doka za ta hau kansu. Alal misali, na biya kudin kujera uku na tsakiya yayin da zan tafi, saboda tare da iyali zan yi tafiyar.

Amman ko da muka zo tasha sai muka taras an cushe wurin ajiyar kaya, babu inda zamu saka ‘yan kananan jakunkunanmu kwara biyu, wadanda idan mun yi tafiya a jirgin sama ba ma auna su, da su muke shiga jirgi, saboda karancin girma ko nauyi da suke da shi. Sai aka nemi wai tunda mu biyu ne kacal a tsakiya, wurin zai ishemu har kayanmu. Ni kuma nace ban amince ba. Daga dukkan alamu kuma sun riga sun sayar da wurin ajiyar kayana, sun karbi sakon kaya wanda shima na samu labarin kudin kujera ake biyansu. Na duba rasitin da aka bani ko akwai lambar wayar ofis sai na kai korafi sai naga in banda sunan na “Adamawa Sunshine” babu komai a jiki, babu lambar waya, babu adireshi! A karshe dai sai saukemu aka yi daga motar, ni da iyalina, na jira wata ta yi lodi bayan sa’a uku, sannan muka kama hanya.

A nan akwai bukatar ace daga cikin jerin masu karbar kudin shiga akwai wadanda suke sa ido wajen ganin an bi ka’ida, an cika alkawari, ko Allah ya sa albarka a harkar da kuma a rayuwarmu baki daya. Wasu shawarwarin da za su biyo baya da za su karfafi wannan, da yardar Allah.

Sunday, 7 May 2023

Yin Waya Fiye Da Minti 30 A Sati Na Kara Hawan Jini —Bincike


Masana kiwon lafiya sun gano cewa yin waya na sama da minti 30 a mako guda na haddasa karuwar cutar hawan jini da kashi 12.

Rahoton da Kungiyar Likitocin Zuciya na Nahiyar Turai ta fitar a ranar Juma’a ya bukaci jama’a da su takaita yin waya domin kare lafiyar zukatansu.

Kamfanin Dillancin Labaran Najeriya (NAN) ya ruwaito cewa rahoton likitocin da aka wallafa a mujallar Digital Health yana nuna yin waya na sama da minti 30 a mako na kara barazanar kamuwa da cutar hawan jina da kashi 12 cikin 100.

Mujallar, wadda a mayar da hankali a kan yadda na’urorin zamani ke shafar lafiyar zuciya, ta ce hakan bai shafi yawan shekarun da mutun ya yi yana amfani da waya ko sanya waya a lasifika ba.

Farfesa Xianhui Qin na Jami’ar Aikin Likita tat Kudancin Guangzhou da ke kasa China, ya kara da cewa masu amfani da waya sun fi mara sa yi yiwuwar kamuwa da hawan jini da kashi 7 cikin 100.

Farfesa Qin ya a halin yanzu kusan biliyan 1.3 masu shekaru 30 zuwa 70 na da hawan jini, wadda ke iya kawo shanyewar barin jiki da kuma mutuwa farat-daya.

Masanin ya bayana cewa “Wayoyin hannu na fitar da maganadisun da ke kara hadarin kamuwa da hawan jini bayan wani lokaci.

“Duk da haka yanayin amfani da waya da ke kawo hawan jini ya bambanta a tsakanin masu kira ko amsawa, da kuma masu tura sakonni ko kuma yin wasanni da ita,” in ji Farfesa Qin.

AMINIYA

Saturday, 6 May 2023

Game Da Tafiya Da Motar Haya A Najeriya Kashi Na Daya

Daga 
Dr. Saidu Ahmad Dukawa

SHIMFIDA
A ranar Talata, 25/4/2023, na shiga motar haya daga Kano zuwa Yola, babban birnin jihar Adamawa a Najeriya. Ranar Alhamis kuma, 27/4/23, na shiga wata motar hayar daga Yola zuwa Jalingo, babban birnin jihar Taraba. Rabona da tafiyar motar haya wacce ta kai tsawan haka tun a shekarun 1983 zuwa 1984 a yayin da na yi hidimar Kasa (NYSC) daga jihar Kano zuwa jihar Bauchi, sai kuma jihar Lagos da na je bayan kammala hidimar kasa a wajejen shekarar 1985.

A wannan karon ma tafiyar ta taso min ne a dalilin wata hidimar Kasar, watau aikin kula da yadda jarrabawar shiga jami’o’i ta kasa (UTME) take gudana. Tun daga lokacin da aka nada Farfesa Is’haq Oloyede a matsayin Magatakardar Hukuma mai tsarawa da gudanar da jarrabawa domin shiga jami’a a Najeriya (JAMB), a shekarar 2016, ya fitar da sababbin tsare-tsare na yadda ake gudanar da wannan jarrabawar. Daga ciki akwai samar da kwamitoci daban daban, har guda goma sha daya (11), domin gudanar da ayyuka daban daban. Guda daga cikin wadannan kwamitoci shine wanda aka lakabawa suna a Turance da “Roving Group”. Watau kwamiti mai kewayawa santocin da ake gudanar da jarrabawa domin kula da yadda jarrabawar take gudana da nufin gano al’amuran da suke bukatar daukar mataki na gaggawa da kuma wadanda za a zauna a tsanake, a yi musu tunani, a samar da yadda za a ingantasu a shekara mai zuwa. Na sami kaina a cikin wannan kwamiti, a inda na shekara biyu ina aiki a Abuja, shekara guda a Adamawa, shekara uku a Kano, bana kuma aka bukaci na je aiki a Adamawa da Taraba.

Abubuwa uku kwamitin da na yi bayaninsa aka dorawa nauyin kula da su, kamar haka:

1. Yanayin tsaro a ciki da kewayen wurin jarrabawa (CBT Centre); saboda Farfesa Oloyede ya karbi aiki a yayin da a ake cikin kamarin kalu-balen tsaro akasa, musamman na ‘yan Boko Haram;

2. Yanayin tantance dalibai masu zana jarrabawa; saboda amfani da fasahar zamani na tantance masu zana jarrabawa (biometrics) da aka shigo da shi; da kuma

3. Yanayin da dakunan da ake gudanar da jarrabawar suke ciki, da inganci da yalwar na’urori masu kwakwalwa (computers); saboda sababbin santoci masu zaman kansu da aka yiwa rajista ta gudanar da jarrabawar.

Amman fa ba akan wannan aikin zan yi bayani ba, saboda aiki ne da ya shafi hukuma, kuma duk wani bayani ita ake turawa ita kuma ta fitar da wanda ya shafi al’umma ta rike na rikewa. Na dan yi wannan tsokacin ne domin a san dan kadan daga irin hidimar da ake yiwa jarrabawa. Zan yi wannan dan takaitaccen rubutun ne akan abubuwa guda biyar:

1. Tsarin daukar fasinja a tasha
2. Halin da wasu tashoshin mota
 suke ciki

3. Halin da titunan Najeriya suke ciki a shekara ta 2023

4. Yanayin tuki da yanayin larurar bukata a yayin tafiya

5. Yanayin tsaro da alakar jami’an tsaro da direbobin mota.

Babban burina da wannan rubutun shine fata da nake da shi na ko Allah ya sa masu ruwa da tsaki su ci karo da rubutun kuma ya sa su inganta al’amura game da abinda ya shafi tafiya a motar haya a Najeriya.
Manya daga cikin masu ruwa da tsaki kuwa sun hada da Kananan Hukomomi (Local Government Authorities), Kungiyoyin sufuri, da na mamallaka motocin haya, da na direbobin haya, da na ‘yan kamasho, da kuma jami’an tsaro, da sauransu. Zan yi kokarin takaita bayani domin gudun kosarwa. Kuma zan raba posting din kashi kashi duk dai saboda gudun kosawa.

(Za a cigaba da magana akan Tsarin Daukar Fasinja a Tashar Mota, da yardar Allah) 

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ayyana karshen annobar Covid-19

A jiya Juma’a ce hukumar Lafiya ta Duniya ta ce an kawo karshen annobar Covid-19, wadda ta yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da wargaza tattalin arziki da sha’anin zamantakewar duniya, sama da shekaru 3 bayan da ta ayyana ta a matsayin annoba. 

Shugaban hukumar Tedros Adhanom Ghebreyesus ne ya sanar da haka a jiya Juma’a, inda ya yi gargadin cewa har yanzu cutar na nan a matsayin barazana.

Wannan mataki na hukumar Lafiyar na zuwa ne bayan da kwamitin kwararru mai zaman kansa da ta nada a game da wannan cuta ta Covid ya ce cutar ba a bukatar mayar da hankali sosai a kan cutar daga hukumar.

Sai dai a cewar Tedros, hatsarin cutar bai kau ba, inda ya yi kiyasin cewa ta kashe sama da mutane miliyan 20 a fadin duniya, kimanin ninki 3 na mutane kusan miliyan 7 da aka ce ta kashe a hukumance.

A ranar 30 ga watan Janairun shekarar 2020 ce hukumar Lafiya ta Duniya ta ayyana cutar Covid-19 a matsayin annoba, makwanni bayan da ta bulla a birnin Wuhan na kasar China.
RFI 

Zaben Adamawa: An Ba Da Belin Kwamishina Hudu

 


’Yan sanda sun bayar da belin Kwamishinan Zabe na Jihar Adamawa da aka dakatar, Hudu Yunusa-Ari, bayan da ya yi kwana uku a tsare a hannunsu.

’Yan sanda sun cafke shi ne kan wata sanarwa mai cike da rudani da ya yi  cewa Sanata Aisha Dahiru Binani ta lashe zaben gwamnan jihar Adamawa, alhali ba a kammala karbar sakamakon karashen zaben ba.

Tun a lokacin INEC ta soke sanarwar, sannan ta bukaci ya gabatar da kansa a hedikwatarta da ke Abuja, amma maimakon ya je, sai ya yi layar zana.

Daga bisani hukumar ta rubuta Shugaban ’Yan Sandan Najeriya wasikar neman ya binciki kwamishinan zaben, kan yamutsa hazon da ya yi.

Amma wata wasika da ya aike wa shugaban ’yan sanda, Hudu ya ce ya yi sanarwar ne a bisa doka, saboda dalilan tsaro.

A ranar Talala ’yan sanda suka sanar cewa sun kama Hudu, wanda ya ce ba ya nadamar sanarwar da ya ya yi cewa Binani ta ci zabe.

Amma kakakin rundunar ’yan sandan Najeriya, Muyiwa Adejobi, ya sanar a ranar Juma’a cewa rundunar ta bayar da belin kwamishinan zaben.

Muyiwa ya cen an umarci Hudu ya rika zuwa hedikwatar rundunar a ranakun aiki domin ci gaba da binciken da ake gudarwa.

AMINIYA

Friday, 5 May 2023

#Hajj2023: Shugaba Buhari Ya Amince Da Cire Kaso 65 Na Kudaden Haraji Da Kamfanonin Jirage Ke Biya

A ci gaba da shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin shekarar 2023, Hukumar Alhazai ta kasa NAHCON ta gana da masu ruwa da tsaki a harkar sufurin jiragen sama a dakin taro na Hajj House dake Abuja. 

A sanarwar da Mataimakiyar Daraktar harkokin hulda da jama’a ta hukumar NAHCON, Hajj2023 Hajiya Fatima Sanda Usara ta fitar, tace an yi hakan ne domin inganta shirye-shiryen da suka kasance masu tasiri wajen jigilar maniyyata Hajji.
 
A taron shirye-shiryen kulla yarjejeniyar jigilar alhaza tare da masu jigilar kayayyaki da aka zaba, Alhaji Zikrullah Kunle Hassan ya bayyana matakan da hukumar ta riga ta dauka na dakile cikas da za a iya samu da zarar an fara jigilar Alhazan 

Shugaban NAHCON ya yi albishir da cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da rage kashi 65 cikin 100 na kudaden sufurin jiragen sama na jiragen sama.
 
Ya kuma sanar da cewa, domin tabbatar da an samar da man jirgi a wadace don jigilar alhazai , NAHCON ta yi shiri da Kamfanin Mai na Najeriya (NNPC) domin kawo karshen hakan. An shawarci masu jigilar maniyyatan da su gana da NNPC da nufin tattaunawa don gujewa matsala 

A cewar shugaban hukumar ta kuma tuntubi masana harkokin sufurin jiragen sama don samun shawarwarin kwararru kuma hukumar za ta ci gaba da bin shawarwarin domin amfanin alhazan Najeriya da kuma kare lafiyar alhazan baki daya 
 
Darakta Janar na Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Najeriya (NCAA), Kyaftin Musa Nuhu wanda ya halarci taron ya bayyana cewa, hukumar tasu ta duba dukkan filayen saukar jiragen sama na Hajji da aka tanada domin samar da tsaro da kayan aiki. Ya yi kira ga wadanda aka zaba da su bi ka’idoji da sharuddan yarjejeniya da za su sanya hannu. An kuma shawarce su da su cika sharuddan da za a fayyace a cikin yarjejeniyoyin domin NCAA a shirye take ta sanya takunkumin karya doka. 

Ya koka da batun jinkiri da soke jigilar jiragen sama kamar yadda aka samu a shekarar da ta gabata, yana mai bayyana hakan a matsayin mai yin tasiri a dukkan ayyukan da ma ya shafi ayyukan Saudiyya ma. A kan wannan cikas na dindindin, tun da farko Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama (GACA) ta gayyaci NCAA don auna irin tasirin da take da shi a ayyukan Hajjin filayen jiragen sama na Madina da Jeddah. Don haka, NCAA ta ษ—ora tsauraran matakai don guje wa sokewa da jinkirin tashin jirgin a wannan shekara.
 
Kaftin Nuhu da sauran masu jawabi a wurin taron sun bayyana damuwarsu kan rufe sararin samaniyar Sudan sakamakon yakin da ake yi a kasar. An bayyana cewa alhazai na iya yin tafiyar sa'o'i bakwai da rabi a kowace tafiya saboda yiwuwar sauya hanya.
 
A wani labarin kuma hudu daga cikin biyar din da aka zaba domin gudanar da jigilar daukar alhazai, sun bukaci karin lokaci kafin sanya hannu kan yarjejeniyar. Dukkansu  kamfanonin jiragen sama ne na cikin gida. 

A cewar ma’aikatan jirgin, akwai bukatar su ci gaba da tuntubar juna da yin lissafin kafin su koma tattaunawa da hukumar ta NAHCON don bayyana amincewarsu ta karshe zuwa ranar Talata 9 ga watan Mayu. 

Sai dai kamfanin FlyNas na Saudiyya ya rattaba hannu tare da nuna shirin fara jigilar Hajji na 2023. Don haka, an ci gaba da ci gaba da aiwatar da tsarin jigilar jirgin tare da FlyNas.
 
Tawagar farko ta aikin Hajji na 2023 da ta kunshi zababbun ma’aikatan NAHCON da ma’aikatan lafiya kadan ne ake sa ran za su bar kasar nan da ranar 21 ga Mayu, 2023.

Kotu ta ษ—aure Ekweremadu shekara tara a gidan yari

An yanke wa wani hamshaฦ™in ษ—an siyasar Najeriya, Ike Ekweremadu, da mai ษ—akinsa, hukuncin ษ—auri a gidan yari bayan kotu a Birtaniya ta same su da laifi kan yunฦ™urin safarar sassan jikin ษ—an'adam.

Kotun ta yanke musu hukuncin ne tare da wani likita "mai shigar musu tsakani" bayan sun kai wani matashi Birtaniya daga Lagos.

Yanzu dai, Sanata Ike Ekweremadu zai shafe kusan shekara goma a gidan yarin Birtaniya.

Sanatan mai shekara 60, da mai ษ—akinsa Beatrice 'yar shekara 56, sun so a cire wa matashin sashen jikinsa ne da nufin dasa wa 'yarsu Sonia 'yar shekara 25, kamar yadda ma'auratan suka bayyana wa Kotun Old Bailey
An kuma samu "mai shiga tsakani" Dr Obinna Obeta da matar sanata Ekweremadu, Beatrice, da laifi

Tun da farko kotu ta samu ma'auratan da likita Dr Obinna Obeta, mai shekara 50, da laifin haษ—a baki don ci da gumin mutumin ta hanyar cire ฦ™odarsa.

Ita ce shari'a ta farko a ฦ™arฦ™ashin dokokin haramta bautar zamani.

Yadda aka kama Sanatan Najeriya bisa zargin yunkurin cire sassan jikin mutum
24 Yuni 2022
Kotu ta samu Ekweremadu da laifin yunฦ™urin safarar sassan ษ—an adam
23 Maris 2023
Matashin da aka yi yunฦ™urin cire wa ฦ™oda domin bai wa ฦดar Ekweremadu
25 Maris 2023
Ike Ekweremadu, wanda alฦ™alin kotun ya bayyana a matsayin "jigon da ya shirya abin da ya faru gaba ษ—aya", zai yi zaman gidan yari tsawon shekara tara da wata takwas.

Hkaa kuma ta yanke wa Dr Obinna Obeta hukuncin ษ—aurin shekara 10 bayan alฦ™alin ya gano cewa shi ne ya samo mutumin da zai ba da gudunmawar wanda matashi ne talaka, kuma mai rauni.

Ita kuma matar sanatan na Najeriya, Beatrice Ekweremadu an yanke mata hukuncin ษ—aurin shekara huษ—u da wata shida saboda yadda ta ษ—an sa hannu wajen aikata laifin.

A wani zaman yanke hukunci da aka nuna ta talbijin, Mai shari'a Justice Johnson ya nunar cewa Ike Ekweremadu, mutum ne da "ฦ™imarsa ta yi matuฦ™ar zubewa".

Ya ce: "Masu fasa-ฦ™waurin mutane a tsakanin ฦ™asashen duniya don cire sassa jikin mutum, abin da suke aikatawa wani nau'in bautar da ษ—an'adam ne."

Mutumin da suka yi safarar tasa, wani talaka ne mai sana'ar tireda a Lagos, da suka kai shi Birtaniya don a cire masa ฦ™oda guda ษ—aya, da nufin dasa wa 'yar Ekweremadu.

Ya dai tsere ne saboda tsoron mutuwa, inda ya kai kansa ofishin 'yan sanda kimanin shekara ษ—aya da ta wuce kuma ya ba da rahoton abin da ya faru, bayan asibitin Royal Free Hospital ya nemi a dakatar da aikin da aka tsara yi a kan kuษ—i £80,000.
BBC