Na shiga matsananciyar damuwa da hare-haren 'yan bindiga a 'yan kwanakin nan - Gwamnan Zamfara

Gwamnan ya bayyana hakan ne a cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na Facebook

Inda yace "A madadin gwamnatin Jihar Zamfara, ina miƙa saƙon ta'aziyya da jaje ga al'ummar ƙaramar hukumar Zurmi, musamman iyalai da ‘yan uwan waɗanda suka rasa rayukansu a harin ta'addanci da 'yan bindiga suka kai garin" 

Ina son tabbatarwa da al'umma cewa gwamnatina za ta bayar da tallafi da agajin gaggawa ga mutanen da abin ya shafa. Sannan ina mai tabbatar da cewa muna nan jajirce akan tabbatar da tsaron rayuka da dukiyoyin al'ummar Zamfara baki ɗaya.

Ina sane da sadaukarwar da jami’an tsaro suke yi a ƙoƙarin da suke na kare rayukan al’umma, gwamnatina za ta ba su duk wasu kayan aiki da kuma tallafin da suka dace domin yaƙar ‘yan bindiga, ba za mu huta ba har sai Zamfara ta samu cikakken tsaro insha Allahu.
 
Waɗannan sabbin hare hare sun biyo bayan nasarar da jami'an tsaro suka samu ne, na kashe shugabannin 'yan ta'addan. Ciki har da nasarar kashe Kachalla Ali Kawaje, Shugaban ‘yan bindiga da ya jagoranci sace ɗaliban jami’ar tarayya dake Gusau.
 
An samu nasarar kawar da shugabannin ɓarayin da dama a wurare daban-daban da suka haɗa da Danjibga, dajin ‘Yar tsakuwa, dajin Munhaye, dajin Kauran Zomo, dajin Dansadau, da kauyen Akuzo.
 
Ina sake jaddada wa al'ummar Jihar Zamfara cewa, da yardan Allah zan ci gaba da bin dukkan matakan da suka dace don tabbatar da zaman lafiya a faɗin jiharmu mai albarka.

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki