Shugaban Majalisar Dokoki Ta Katsina Ya Raba Tallafin Naira Miliyan 35

Kakakin Majalissar Dokoki ta Jihar Katsina, Nasir Yahaya, ya bayar da tallafin Naira Million Talatin da Huɗu da Dubu Ɗari Tara da Hamsin. (34,950,000) ga Mutum Dubu Ukku (3000) a filin wasan Ƙwallon Kafa dake Daura

Hadimin tsohon Shugaban Najeriya, Buhari Sallau, ya rawaito a shafinsa na Facebook cewa, an bayar da Tallafin ga Marayu, Limamai, Zawarawa, Masu Ƙananan Sana'oi, Exco, Mata, Matasa, Students, yan Media, Dagattai, Mabuƙata, yan siyasa, Ƙungiyar Teloli, Ƙungiyar Masu Shayi da Masu chajin waya, da sauran su. Inda ko wanne daga cikinsu zai amfana da Tallafin, Naira Dubu Goma (10,000)

Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Radda PhD, yayi Jin-Jina gami da fatan Alkhairi ga Kakakin Majalissar akan wannan abin Alkhairi da yayi, sannan yayi roƙo gami da Jan hankali ga wanda suka amfana da wannan Tallafin da suyi amfani dashi ta hanyar daya dace, domin su bunƙasa Kasuwar su. 

Haka kuma Mataimakin Shugaban Jam'iyyar APC na Jihar, Alh. Bala Abu Musawa, ya taya mutanen Daura murna, bisa ga Jajirtaccen Shugaba da suka samu.

Taron ya samu Halartar Tsohon Shugaban Ƙasar Nigeria, Gen. Muhammadu Buhari, Gwamnan Jihar Katsina, Malam Dikko Umaru Raɗɗa PhD, Shugaban Jam'iyyar APC na Jiha da Mataimakinsa, Yan Majalissar Dokoki ta Jihar Katsina, kwamishinoni da masu bada shawara, Wakilin Mai Martaba Sarkin Daura, Hajia Ambarud Sani Wali, Shugaban karamar hukuma, Tsofaffin yan Majalissar Jiha, Barr. Ahmad Usman El-Marzuq, da sauran manyan baƙi

Kakakin Majalissa ya bayar da kyautar Sa (Bijimi) ga Muhammadu Buhari, da kyautar Doki ga Gwamna Malam Dikko Umaru Raɗɗa. 
 
Sannan Ƙungiyoyin Daura Forum, DECA, DEDA, Health and Education Department, Ƙungiyoyin Addini, da Babbar Ƙungiyar, Daura Consortium sun bayar da Lambobin Yabo da Girmamawa (Award) ga Mai Girma Kakakin Majalissar Dokoki a bisa ayyukan Alkhairin da yake aikatawa ba dare ba rana a Daura

Haka zalika Ƙungiyar Daura Forum ta bada lambar yabon ga  Muhammadu Buhari, da Gwamna Malam Dikko Umaru Raɗɗa  

Daga karshe Kakakin Majalissa yayi Godiya ga manyan baƙi da suka halarci wannan Babban taron, sannan yayi Addu'a da fatan Allah ya maida kowa gidanshi lafiya, l

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki