Yanzu-Yanzu: Zulum ya amince da nadin Mohammed Dawule a matsayin mai rikon Hukumar Alhazai ta Jahar Borno

Gwamnan jihar Borno, Babagana Umara Zulum, ya amince da nadin Mohammed Dawule Maino a matsayin mukaddashin sakataren hukumar jin dadin alhazai ta jihar Borno.

An bayyana nadin ne a ranar Lahadin da ta gabata a wata sanarwa da sakataren gwamnatin jihar Borno, Hon. Bukar Tijjani.

Sakataren gwamnatin jihar ya kara da cewa nadin wanda ya fara aiki nan take, ya dogara ne akan cancanta da kuma bayanan shekarun baya a aikin gwamnati.

Har zuwa lokacin da Dawule ya nada shi mamba ne a sabuwar Hukumar Ilimi ta Larabci da Sangaya ta Jihar Borno (BOSASEB. Kafin nan, Dawule ya yi aiki a Ma’aikatar Ilimi ta Jihar Borno tsakanin 2015 zuwa 2022.

Ya kuma yi aiki a Makarantar Sakandare ta islamiyya da ke Maiduguri da Kwalejin Gwamnati da ke Maiduguri da kuma Makarantar Alkur’ani ta Model da ke Konduga.

An haifi Mista Dawule mai shekaru 50 a duniya a karamar hukumar Kaga da ke arewacin jihar Borno.

Gwamna Zulum ya taya Mohammed Dawule Maino murna sannan ya ce yana fatan ci gaba da yi masa hidima tare da nagartar al’ummar jihar Borno.

Insight Northeast 

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki