Yanzu-Yanzu: Ganduje ya sake nada Aminu Hikima sabon mukami a matakin kasa

A cikin sanarwar da Aminu Dahiru Ahmed ya fitar a shafinsa na Facebook, ya ce, wannan shi ne karo na hudu da Baba Ganduje ya nada ni. A lokacinsa na farko a matsayin gwamnan jihar Kano, ya nada ni babban mai taimaka masa na musammam kan harkokin daukar hoto. Haka kuma a wa’adinsa na biyu ya sake nada ni a Wannan matsayi.
 
Lokacin da ya bar ofis bayan shekaru takwas, ya nada ni mai daukar hotonsa na kashin kai. Nadin na baya-bayan nan shi ne na hudu.
 
Aminu Dahiru yace Baba Ganduje ya yi min abin da uba kawai zai yi wa dansa. Ya dauki nauyin karatuna da sauran abubuwa da yawa. "Wacce irin ni'imomin Ubangijinku kuke karyatawa"?

A matsayina na mai daukar hotonsa, ina da abubuwa da yawa da zan ce game da Baba Ganduje. Mai daukar hoto yana aiki tare da maigidansa. Ni ma na yi aiki tare da Baba Ganduje tsawon wadannan shekaru. Ina shaidawa tsohon gwamnan yana da riko da addini, mai tausasawa, mai kirki, mai yarda da mutuntawa har da wadanda ke karkashinsa. Kasancewara da Baba Ganduje ya kawo min sauyi ta fuskoki da dama.
 
Bangaren addini na Baba Ganduje yana da ban sha'awa. Ku yi aiki da Baba Ganduje, tabbas za ku samu yin koyi da  al'adar yin addu'o'in ku a kan lokaci, kuma ku yi ayyukanku na addini cikin aminci.
 
Baba Ganduje ya shahara wajen gina masallatai, makarantun Islamiyya, shirya gasar karatun Alkur’ani da daukar nauyinsu da musulunta. Ganduje ya zuba jari mai yawa ga marasa galihu.
 
Mataimakin na musammam ga Shugaban jam'iyyar APC ta Kasa, ya ci gaba da cewa, A siyasance Baba Ganduje shi ne ainihin ma’anar dan siyasa. Shi ne gwanin da ke bayyana siyasar zamani. Abin sha'awa Baba Ganduje yana yafiya don Allah. Yana ramuwar gayya ne kawai akan cin zarafin da aka yi masa a siyasance.
 
Ta fuskar karfafawa mutane, Aminu yace Ganduje mai baiwa ne ajin farko, wanda yake yi a boye. Zai ba ku, ya sake ba ku kuma ya tambaye ku kada ku gaya wa kowa. Wannan mai bayarwa ne na gaske.
 
Wadannan kyawawan halaye da na lissafo su a sama sun fi su Baba Ganduje da Allah Ta’ala ya karawa rayuwa lafiya, arziki, iyali da mulki. Siffofin guda É—aya suna zama kagara tsakaninsa da masu zaginsa.
 
Allah Ta'ala Ya ci gaba da kasancewa tare da shi, Ya kuma kare shi daga dukkan sharrin masu makirci. Amin.

Na gode Baba!

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki