Posts

Showing posts from April, 2023

Gyara a dokar aikin Hajji zai rage tsadar tafiya Makkah a Najeriya - Sanata Dan Baba

Image
Dan Majalisar Dattijai mai wakiltar Sokoto ta Kudu a Majalisar Dokokin Najeriya Sanata Ibrahim Abdullahi Dan Baba ya sha alwashin yin duk abin da zai iya wajen ganin an yi wa dokar aikin Hajji kwaskwarima a sabuwar majalisa ta goma da za ta fara aiki. Sanatan wanda ya kasance a tsohuwar majalisa ta tara wacce za ta gama aikinta cikin watan Mayun shekaran nan ta 2023 ya ce tun da farko ya gabatar da kudurin gyaran a gaban majalisar mai karewa. Sanata Dan Baba ya kara da cewa lokaci ya yi da ya kamata a samar wa mahajjata sauki wajen biyan makudan kudade domin aikin Hajji. A cewar dan majalisar, yin gyara ga dokar Hukumar Aikin Hajji ta kasar shi ne zai magance yadda ake samun karuwar kudin tafiya Hajjin.  Ya ce ya bukaci majalisa ta gudanar da bincike kan badakalar da ke cikin aikin Hajji a Najeriya kuma majalisar ta kafa wani kwamitin bincike. "Biciken ya gano ana sama da fadi da kudaden mahajjata, otel da ya kamata a kama na kwana arba'in sai a kama na tsawon kwan

APC Group Calls For All Stakeholders To Consider Senator Barau As Next Senate President

Image
Kano Chapter of APC national supporters center calls for all stakeholders to consider senator Barau Jibirin as the next Senate president of the 10th Senate. In a statement signed by its State Coordinator, Aliyu A Aliyu, the Group argued that his widespread acceptance, pragmatic leadership skills have made him the best to be considered as the next Senate president. Accordingly his perfection to duty especially as Chairman Senate committee on appropriation defined his competency. North West support for APC especially Kano that produced about two million votes in 2015,over a million votes in 2019 and five hundred and thirteen thousand votes this year need to be considered by the party's leadership in the incoming administration of Bola Ahmed Tinubu. The Group advice APC and the president elect not to neglect Kano by doing so it can jeopardize the party chances in the future. It called on senators to support Barau Jibirin in his effort to bring about purposeful leadership.

Wutar Lantarki: Katse Layin KEDCO A Kano Somin-Tabi Ne —TCN

Image
Kamfanin Samar da Wutar Lantarki na Kasa (TCN) ya ce katse wutar da ya yi wa Kamfanin Rarraba Wutar Lantarki na KEDCO a Jihar Kano somin-tabi ne. Wasu sassan Jihar Kano sun yi kwanaki a cikin duhu bayan TCN ya katse layin wutar da suke kai saboda taurin bashin da yake bin KEDCO. TCN ya katse wasu layikan wutar KEDCO mai kula da jihohin Kano da Jigawa da Katsina bayan kokarinsa na ganin kamfanin ya biya bashin ya faskara. Mataimakin Janar-Manajan TCN na Shiyyar Kano, Bello Muhammad da kuma kakakin KEDCO, Sani Bala Sani, sun tabbatar cewa TCN ya katse wutar a ranar 26 ga watan Afrilu da muke ciki. Layukan wutar da TCN ya kashe a Kano su ne Club Road da CBN da kuma Flour Mills (Dan Agundi), wanda hakan ya jefa yankunan da ke samun wuta daga nan a cikin duhu na tsawon kwanaki. Tun ranar 24 ga watan ranar 24 ga wata Babban Jami’in Kasuwanci na TCN, E. A. Eje ya sanar cewa, “TCN ya ba da umarnin katse wutar KEDCO saboda saba ka’idar biyan bashi.” Ya bayyana cewa katse layikan so

Gwamnatin Tinubu Ce Za Gudanar Da Kidaya —Buhari

Image
  Shugaba Muhammadu Buhari ya amince a dage lokacin gudanar da Kidayar Jama’a da Gidaje da aka shirya farawa ranar 3 ga watan Mayu mai kamawa. Kwana hudu kafin fara aikin Buhari ya ce ya bai wa gwamnati mai jiran gado damar yanke shawara kan lokacin gudanar da kidayar domin tabbatar da nasararsa. Ya sake dage lokacin gudanar da kidayar ne bayan wata ganawa da tsakanin Shugaba Buhari da shugaban hukumar, Nasir Isa Kwarra tare da Majalisar Zartarwa ta Tarayya a ranar Juma’a a Fadar Shugaban Kasa. Sanarwar da Ministan Yada Labarai da Raya Al’adu, Lai Mohammed ya fitar ta ce duk da haka Shugaba Buhari ya jaddada muhimmancin gudanar da kidayar wadda rabon da a gudanar shekara 17 ke nan. Shugaban ya kuma yaba da kyakkyawatan shirin da hukumar ta yi wa kidayar, wanda zai tabbatar da ingancinsa kamar na sauran kasashen duniya. Wata majiya a hukumar ta ce an dage aikin kidayar ne saboda wasu matsalolin da hukumar ke fuskanta da za su hana ta gudanar da aikin a lokaci guda; sai dai ba ta yi kari

’Yan Bindiga Sun Sako 70 Daga Cikin Yara 85 Da Suka Sace A Zamfara

Image
  ’Yan ta’adda da suka yi garkuwa da yara sama da 85 a Jihar Zamfara sun sako 70 daga cikin yaran, amma sun kashe biyu. A ranar Juma’a ’yan ta’addan suka sako yaran, kimanin mako uku bayan sun sace su daga kauyen Wanzamai na Karamar Hukumar Tsafe ta jihar. Wani mazaunin yankin Sani Aliyu ya ce, “Yara biyu da ’yan bindigar suka kashe sun yi kokarin tserewa ne, wadanda aka sako din kuma sun galabaita saboda tsananin yunwa, kuma yanzu ana duba lafiyarsu.” Ya ce ganin irin galabaitan da yaran suka yi ya sa iyayensu koke-koke, kuma “An sako su ne bayan an biya kudin fansa Naira miliyan shida; da farko miliyan uku aka ba su, amma suka ki sako su, sai an kara musu da sabbin babura guda biyu.” Sai dai ya bayyana cewa duk da haka, akwai karin wasu yaran a hannun ’yan ta’addan, “ba mu san dalilin da suka ki sako su ba.” Wakilinmu ya yi kokarin jin ta bangaren Rundunar ’Yan Sandan Jihar Zamfara, amma hakarsa ta yin magana da kakakin rundunar, CSP Muhammad Shehu, ba ta cim ma ruwa ba. Kimanin mako

Ba Ma Yi Wa Shirin Mika Mulki Zagon Kasa - Ganduje

Image
Gwamnatin jihar Kano  ta ce a shirye take domin miÆ™a mulki ga sabuwar gwamnati cikin ruwan sanyi ba tare da tayar da Æ™ura ba. Cikin wata sanarwa da ta fitar mai É—auke da sa hannun kwamishinan yaÉ—a labarai Muhammad Garba, gwamnatin ta ce tuni aka samar da babban kwamiti da kuma Æ™anana da za su taimaka domin ganin an miÆ™a mulkin salin alin. Ya musanta iÆ™irarin jam’iyyar NNPP da ta ke jiran karÉ“ar mulki na cewa gwamnatin Ganduje na yi wa shirin miÆ™a mulki zagon Æ™asa. Kwamishinan ya Æ™ara da cewa kwamitin miÆ™a mulki na É“angaren gwamnatin Ganduje na rubuta rahoton Æ™arshe kafin miÆ™a mulki. Ya bayyana cewa kamata ya yi kwamitin karÉ“a na gwamnati mai jiran gado shi ma ya shirya domin karÉ“ar rahoton, wanda ya yi alÆ™awarin miÆ™awa a kan lokaci. Muhammad Garba ya Æ™ara da cewa manufar miÆ™a mulki shi ne gwamnati mai sauka ta miÆ™a duk wasu abubuwa na tafiyar da shugabanci cikin ruwan sanyi. Ba yunkurin yaÉ—a wani tunani ko wata aÆ™ida ba. Ya kuma ce kamata ya yi gwamnati mai jiran gado ta ma

Labari da dumiduminsa : Shugaba Buhari Ya Dage Kidayar 2023

Image
A wata ganawa da ya yi da mambobin majalisar zartaswa ta tarayya da kuma shugaban hukumar kidaya ta kasa, shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da dage kidayar yawan jama’a da gidaje na shekarar 2023, wadda aka shirya gudanarwa tun daga ranar 3-7 ga watan Mayun 2023. Za a tantance sabon ranar ne ta hanyar gwamnati mai shigowa. An cimma matsayar ne bayan taron ya jaddada muhimmancin da ke akwai na kidayar jama’a, wanda ba a yi ta tsawon shekaru 17 ba, na tattara sabbin bayanai domin inganta rayuwar ‘yan Nijeriya, da kuma fitar da manufofin ci gaban kasar. Duk da irin gagarumin ci gaban da aka samu da suka hada da kammala aikin tantance yankin da kuma daukar ma'aikata da horar da ma'aikata, shugaban ya bayyana cewa kamata ya yi gwamnati mai jiran gado ta samu damar karfafa wadannan nasarori. Shugaba Buhari ya yaba wa tsarin hukumar kidaya ta kasa, musamman yadda ake tura na’urorin zamani domin tabbatar da kidayar jama’a mai inganci kuma abin dogaro. An umurci hukum

PDP Ta Bukaci Sanyawa Buhari Takunkumi

Image
Babbar jam’iyyar adawar Najeriya ta PDP ta bukaci kasashen duniya da su hana shugaban kasa Muhammadu Buhari bizar tafiye tafiye da zaran ya mika mulki ranar 29 ga watan gobe, saboda abinda ta kira kalamansa dangane da zaben shugaban kasar da akayi ranar 25 ga watan Fabarairu.  Yayin tsokaci akan zaben, Buhari ya bayyana ‘yan adawar Najeriya a matsayin wadanda suka shantake akan cewar zasu samu nasara ba tare da neman goyan bayan jama’a kamar yadda jam’iyarsa ta APC tayi ba.  Sakataren hulda da jama’a na jam’iyyar Debo Ologunagba yace kalaman shugaban na iya tinzira jama’a da kuma haifar da illa ga zaman lafiyar kasar.  Ologunagba ya kuma ce kalaman na iya karfafawa alkalai gwuiwa wajen yanke hukunci akan karar da suka shigar a gaban kotu domin kalubalantar sakamakon zaben wanda yace tuni wasu a ciki da wajen kasar ke bayyana shi a matsayin mafi muni a tarihin Najeriya.  Jam’iyyar PDP tace zaben da akayi bana ya gamu da matsalolin da suka sabawa kundin tsarin mulkin kasa da

Ci-da-zucin 'yan adawa ne ya kayar da su zaɓe - Buhari

Image
Shugaba Muhammadu Buhari ya ce ya yi imani ci-da-zuci ne babban abin da ya janyo taron 'yan adawar Najeriya suka sha kaye a zaɓen shugaban ƙasa da ya wuce. Ya bayyana haka lokacin da ya karɓi gwamnonin jam'iyyarsa ta APC a ƙarƙashin jagorancin Gwamna Abubakar Atiku Bagudu na jihar Kebbi. Yana cewa a daidai lokacin da jam'iyya mai mulki take aiki tuƙuru don ci gaba da mulki a zaɓukan da aka yi a baya-bayan nan, 'yan adawa suna can sun cika da ci-da-zuci. "Sun je suna ta faɗa wa masu goya musu baya a ƙasashen waje cewa, sai sun kayar da APC. Yayin zaɓen na 25 ga watan Fabrairu, ɗan takarar jam'iyyar APC mai mulki Bola Ahmed Tinubu ya smau ƙuri'a 8,794,726. Sai Atiku Abubakar, tsohon mataimakin shugaban ƙasar da ya samu ƙuri'a miliyan 6,984,520. Ɗan takarar jam'iyyar Labour, Peter Obi yana da ƙuri'a miliyan 6,101,533, yayin da tsohon gwamnan Kano, Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso ya zo na hudu da ƙuri'a miliyan 1,496,687. Shugaba Bu

Kwamitin Karbar Mulki Na NNPP Na Kano Ya Zargi Gwamna Ganduje da gurgunta Tsarin Karbar mulki

Image
Kwamitin Karbar Mulki na jam’iyyar NNPP reshen jihar Kano, ya zargi gwamnatin Gwamna Abdullahi Umar Ganduje mai barin gado da yin zagon kasa ga tsarin mika mulki ga gwamnatin Injiniya Abba Kabir Yusuf mai jiran gado. A cewar shugaban kwamitin mika mulki na jam’iyyar NNPP, Farfesa Abdullahi Baffa Bichi, gwamnatin Ganduje ta nuna turjiya da rashin hadin kai tun bayan kafa kwamitin mika mulki na NNPP da zababben gwamna Abba Kabir Yusuf ya yi. Jaridar Nigerian Tracker ta rawaito Bichi yana bayyana cewa kwamitin mika mulki na NNPP ya kafa kananan kwamitoci 33, amma babu daya daga cikin kwamitocin da ya samu hadin kai daga gwamnatin Ganduje. Duk da yunkurin kwamitin mika mulki na jam’iyyar NNPP na shirya taron hadin gwiwa da kwamitin mika mulki na gwamnati mai barin gado, gwamnatin Ganduje ta bukaci su zabi mutane uku ne kawai a taron wanda jam’iyyar NNPP ba ta amince da shi ba. Bichi ya zargi Gwamna Ganduje da mayar da dukkan sakatarorin dindindin na jihar a wani bangare na koka

Kotu ta sake umartar Ganduje da ya amince da Muhuyi Magaji a matsayin Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa

Image
Kotun ma'aikata ta kasa da ke zamanta a Kano ta yi watsi da karar farko da gwamnatin jihar Kano ta shigar kan wata doka da ta hana gwamnatin jihar nada kowane mutum a matsayin shugaban hukumar yaki da cin hanci da rashawa ta jihar. Idan dai za a iya tunawa, a kwanakin baya ne Gwamna Abdullahi Umar Ganduje ya mika sunan mukaddashin shugaban hukumar Mahmud Balarabe ga majalisar dokokin jihar domin tabbatar da shi a matsayin kwararren shugaba. Majalisar ta tsara tantance shugaban riko a ranar 2 ga Mayu, 2023. SOLACEBASE ya bayar da rahoton a wani hukuncin da kotu ta yanke a baya a cikin wani umarni na musamman cewa dakataccen shugaban hukumar korafe-korafen al’umma da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, Muhuyi Magaji Rimigado ya ci gaba da kasancewa a matsayin shugaban hukumar. Biyan kuÉ—i zuwa wasiÆ™armu Shigar da adireshin imel É—in ku Yi rijista Karanta kuma:Kwarai Muhuyi a matsayin Shugaban Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Kano- Kotu ta umarci Ganduje A zam

HAJJIN 2023: Rikicin Sudan Ka Iya Kawo Matsala Ga Jigilar Ahazan Najeriya - Kungiyar Fararen Hula

Image
Rikicin da ake fama da shi a kasar Sudan na iya kawo cikas ga jigilar maniyyatan Najeriya zuwa kasar Saudiyya cikin sauki, domin gudanar da aikin hajjin shekarar 2023, in ji kungiyar daukar rahotannin aikin hajji mai zaman kanta.   Kungiyar farar hula a cikin wata sanarwa da ta fitar a ranar Juma'a mai dauke da sa hannun shugabanta na kasa Ibrahim Muhammad, ta ce tuni yakin ya kai ga rufe sararin samaniyar Sudan ba zato ba tsammani.   Kungiyar ta ce Najeriya "dole ne ta hanyar NAHCON ta yi gaggawar sake duba kalubalen da ke gabanta sannan ta fito da wasu zabin da za a yi a matsayin ma'auni."   Kamar yadda jadawalin NAHCON ya nuna, za a fara jigilar maniyyatan Najeriya zuwa kasa mai tsarki a ranar 21 ga Mayu, 2023.   Jiragen saman jigilar alhazan Najeriya na tafiya ta sararin samaniyar Sudan a lokacin da suke tafiya Saudiyya, kuma ana daukar matsakaicin sa'o'i hudu zuwa biyar kafin su isa kasar.   Sai dai kuma rufe sararin samaniyar kasar Sudan ba z

Firaministan Pakistan ya tsallake rijiya da baya

Image
  Firaministan Pakistan Shehbaz Sharif ya tsallake rijiya da baya, bayan da ‘yan majalisar kasar suka kada kuri’ar yanke kauna, yayin da sauran kungiyoyin fararen hula suka matsa kan a fara shirin gudanar da babban zaben kasar.  Sharif ya sami kuri’un amincewa guda 180, yayin da ‘yan majalisa 172 suka nuna rashin amincewa da salon shugabancin sa, abinda ya bashi damar ci gaba da rike mukamin sa da kyar.  Ko da yake jawabi, kakakin majalisar dokokin kasar Raja Pervais Asharf, yace a yanzu abinda majalisar zata mayar da hankakli shine batun babban zaben da ke tafe.  Sharif wanda ya gaji Imran Khan ya yabawa mambobin jam’iyyyar sa da ke majalisar bayan da suka amince da salón mulkin sa, tare da yanke hukuncin sake bashi dama, ta hanyar kada kuri’ar amincewa da shi.  rfi

An tilasta wa 'ya'yanmu ba da fasfo kafin a kai su Masar - Iyayen É—aliban Sudan

Image
  Hausawa kan ce tsuguno ba ta Æ™are ba a kan lamarin É—aliban Najeriya da ke karatu a Sudan, waÉ—anda gwamnatin Najeriyar ta ce za ta kwaso su zuwa gida. Yayin da ake kukan cewa har yanzu akwai tarin É—alibai da aka bari a Æ™asa - a gefe É—aya kuma iyayensu na kukan lokaci na Æ™urewa, ko da yake an tsawaita yarjejeniyar tsagaita wuta da Æ™arin sa'a 72. Iyayen É—alibai da dama da BBC ta tattauna da su, sun ce yanzu haka halin da yaransu ke ciki ya fi wanda suka baro a Khartoum. Asma'u Yarima Muhammad, sakatariyar Æ™ungiyar iyayen É—aliban Najeriya da ke karatu a Sudan, ta ce 'ya'yanta biyu "na cikin tsakiyar sahara ba tare da sanin inda suka dosa ba". Asma'u Yarima na da yara biyu 'yan shekara 18, wato 'yan tagwaye ne duka maza. Daya na karantar fannin zane, sai kuma É—ayan da ke nazarin aikin likita. Ta ce yawancin dare sukan yi waya da yaranta irin ta iyaye da 'ya'ya wadda rabinta nishaÉ—i ne, É—aya rabin maganar karatu. Amma tun daga 15 ga watan Afril

Muhuyi Magaji Ya Karbi Naira Miliyan Biyar Da Dubu Dari Biyar Bayan Da Kotu Ta Tursasa Gwamna Ganduje

Image
Tsohon shugaban hukumar korafe-korafe da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, Muhuyi Rimingado, ya karbi kudi naira miliyan 5,713,891.22 daga asusun albashi na gwamnatin jihar Kano. Mista Rimingado ya tabbatar da karbar kudin ne a ranar Alhamis, inda ya ce zai yi amfani da wani bangare na su ne don bayar da agaji. A ranar Talata, kotun ma'aikata ta kasa, Abuja ta umarci GTBank da ya biya Mista Rimingado bashin albashin ma’aikata daga asusun gwamnatin jihar, biyo bayan dakatarwar da Gwamna Abdullahi Ganduje ya yi ba bisa ka’ida ba a watan Yulin 2021. Jaridar DAILY NIGERIAN ta ruwaito cewa gwamnan ya dakatar da Mista Rimingado ne bayan ya bude bincike kan wasu kwangiloli da ake zargin an baiwa wasu kamfanoni masu alaka da iyalan gwamnan. A zaman da aka ci gaba da yi a ranar Talatar da ta gabata, bankin ta bakin lauyansa Joshua Shekwolo ya shaida wa kotun a cikin wata takardar rantsuwa cewa gwamnatin jihar Kano ta na da asusun ajiyar banki da jimillar kudaden da suk

Shugaban NAHCON Ya Kaddamar Da Tawagar Ma'aikatan Lafiya Na Hajin 2023

Image
Hukumar alhazai ta kasa NAHCON, ta gudanar da aikin tantance tawagar likitocin da zasu kula da alhazai a aikin hajjin na shekarar 2023.  A sanarwar da Mataimakiyar Daraktar harkokin hulda da jama’a ta hukumar Hajiya Fatima Sanda Usara ta fitar, tace an  gudanar da taron ne a yau, 27 ga Afrilu, 2023 tare da kusan masu neman 212 da aka gayyata don tantancewa. Manyan jami’ai karkashin jagorancin Dakta Usman Galadima na Ma’aikatar Lafiya ta Tarayya, wanda kuma shi ne Shugaban Ma’aikatan Lafiya na Hukumar Kula da Lafiya ta Kasa (NMT), sun tantance takardun kwararrun likitoci, masu harhada magunguna da ma’aikatan jinya da za su kafa tawagar NMT. Da yake gabatar da jawabinsa a lokacin kaddamar da yan tawagar da wayar da kan jama’a, Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, Shugaban Hukumar NAHCON ya taya ‘yan tawagar guda 230 murna wanda aka zabo su daga cikin  mutane sama da 10,000 da suka nema  Ya umarce su da su dauki zabarsu a matsayin amana daga Ubangiji Madaukakin Sarki, wanda suke amf

Labari Da Dumiduminsa : Gwamnatin Tarayya Ta Dakatar Da Shirinta Na Janye Tallafin Man Fetur

Image
Gwamnatin tarayya ta dakatar da shirin cire tallafin man fetur a karshen gwamnatin shugaba Muhammadu Buhari. Wannan na daga cikin shawarar da majalisar tattalin arzikin kasa ta yanke a zamanta na ranar Alhamis. Ministar Kudi, Kasafin Kudi da Tsare-Tsare na Kasa, Misis Zainab Ahmed ce ta bayyana hakan a lokacin da take zantawa da manema labarai a fadar shugaban kasa a karshen taron hukumar zaben da mataimakin shugaban kasa Yemi Osinbajo ya jagoranta a fadar shugaban kasa da ke Abuja. Zainab ta bayyana cewa akwai yiyuwar cire tallafin zai fara aiki a watan Yuni saboda dokar masana'antar man fetur, PIA da kuma kasafin kudin 2023 sun ba da tallafi har zuwa watan Yuni, don haka duk wani jinkiri na iya buƙatar gyara PIA da tanadin kasafin kuɗi. Ministan, ya ce babu wani wa'adi da aka bayar na cire tallafin, kuma gwamnati mai zuwa za ta yanke shawara a kan lokacin da za ta iya yin hakan. Cikakken labarin zai zo muku nan gaba kadan

Saudiyya Ta Kwashe ’Yan Najeriya Da Suka Makale A Sudan Zuwa Kasarta

Image
Gwamnatin kasar Saudiyya ta kwashe wasu daga cikin ’yan Najeriya da suka makale a yakin da ya barke a Sudan zuwa kasarta. Minista a Ma’aikatar Harkokin Waje ta Najeriya, Zubairu Dada, ya ce Saudiyya ta tura jiragen ruwa da suka kwashe ’yan Najeriya zuwa birnin Jeddah na kasarta, bayan barkewar yaki a Sudan. Ma’aikatar ta ce daga bisani za a maido da ’yan Najeriyan da aka kai Saudiyya gida, kuma gwamnatin Tarayya na kokarin ganin cewa babu dan Najeriya ko daya da ya rage a Sudan kafin cikar wa’adin awa 72 da bangarorin da ke yaki da juna suka bayar na tsagaita wuta. Ta bayyana cewa a kokarinta na kwashe ’yan Najeriya da suka makale bayan barkewar yakin, Gwamnatin Tarayya ta kashe Naira miliya 552 kan daukar hayar motocin da za su fitar da su zuwa iyakar Sudan da kasar Masar. Ministan Harkokin Waje na Najeriya, Geoffrey Onyema, ya ce an dauki hayar bas-bas 40 da za su kwashi ’yan Najeriya daga Khartoum, babban birnin Sudan zuwa iyakar kasar Masar da ke Aswan, inda za su hau jirgi zuwa gi

Buhari Ya Je Wurin Fareti Sanye Da Kakin Soja

Image
Shugaban Kasa Muhammadu Buhari ya fito sanye da kakin sojoji a dandalin Eagles Square inda sojoji ke fareti a safiyar Alhamis.  Buhari ya isa dandalin, inda sojoji 1,000 ke gabatar da fareti inda ya samu rakiyar Shugaban Ma’aikatan Fadar Shugaban Kasa, Ibrahim Gambari. Babban Hafsan Taron Najeriya, Janar Lukcy Irabor da Babban Hafsan Sojin Kasa, Laftanar-Janar Faruk Yahaya da kuma Shugaban ’Yan Sandan Najeriya, Usman Baba na daga cikin mahalarta faretin. Sauran hafsoshin tsaro da Shugaban Majalisar Dattawa, Ahmad Lawan na daga cikin mahalarta faretin sojojin. AMINIYA

Labari Da Dumiduminsa : Hukumar NAHCON Ta Bayar Da Awa 48 Ga Hukumomin Alhazai Na Jihohi Dasu Sanya Kudaden Alhazansu

Image
Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya, NAHCON, Alhaji Zikrullah Kunle Hassan ya ba da ranar Juma’a 28 ga watan Afrilu a matsayin wa’adin tura kudin aikin Hajjin shekarar 2023 daga hukumomin kula da jin dadin Alhazai na Jihohi.  A sanarwar da Mataimakiyar Daraktar harkokin hulda da jama’a ta hukumar, Hajiya Fatima Sanda Usara ta sanyawa hannu, shugaban Ya bayyana hakan ne a yau 26 ga watan Afrilu 2023 a yayin wani gagarumin taro da shugabannin hukumomin jin dadin alhazai na Jihohi a hedikwatar Hukumar ta NAHCON.  Taron dai an yi shi ne domin tattauna muhimman batutuwan da suka shafi kudaden da maniyyata ke aikawa da maniyyata aikin Hajji domin kammala yawan wadanda suka cancanci zuwa aikin hajjin 2023 daga Najeriya.  A cewar Alhaji Zikrullah Kunle Hassan, hukumar za ta yi farin cikin yin aiki da duk wani kudi da za ta aika kafin ranar Juma’a, sannan ta rattaba hannu kan yarjejeniyoyin jigilar jirage zuwa Saudiyya a shekarar 2023 bisa ga wannan adadin.  Ya bayyana cewa ana sa

Yanzu-yanzu: Tsohon Minista, Musa Gwabade ya rasu

Image
Tsohon ministan kwadago da wadata, kuma jigo a jam’iyyar PDP, Alhaji Musa Gwadabe ya rasu. Gwadabe ya rasu ne a Kano yana da shekaru 86 a daren ranar Talata, bayan doguwar jinya, kamar yadda jaridar SOLACEBASE ta ruwaito. Dan uwan ​​marigayi dattijon jihar, Nasiru Gwadabe ya shaida wa SOLACEBASE cewa za a yi sallar jana'izar marigayin da misalin karfe 2:00 na rana a yau Laraba a gidansa da ke kan titin Maiduguri a Kano. Biyan kuÉ—i zuwa wasiÆ™armu Shigar da adireshin imel É—in ku Yi rijista Karanta Hakanan: PSC ta amince da tura sabbin CPs zuwa jihohin Kano, Katsina 9 sauran jihohi, FCT Alhaji Musa Gwadabe wanda ya rike mukamin minista a lokacin Olusegun Obasanjo na farko daga shekarar 1999 zuwa 2003 ya kuma kasance sakataren gwamnatin jihar Kano a zamanin marigayi Sabo Bakin Zuwo kuma ya kasance mamba a kwamitin gudanarwa da dama. Har zuwa rasuwarsa dan jam'iyyar All Progressives Congress, APC ne kuma shugaban hukumar kula da harkokin horar da masana'antu, ITF. Ya

Kotu ta umarci Bankin Guarantee Ya Biya N5.7m Da Muhuyi Rimingado Daga Asusun Gwamnatin Kano

Image
Kotun ma'aikata ta kasa da ke Abuja ta umarci Bankin (GT) da ya biya korarren shugaban hukumar KORAFE-KORAFE jama’a da yaki da cin hanci da rashawa ta jihar Kano, Muhuyi Rimingado, kudi N5,713,891.22 daga asusun albashi na gwamnatin jihar. Adadin kudaden da  Rimingado ke bin gwamnatin ne na albashin ma’aikata, bayan dakatar da shi a watan Yulin 2021. DAILY NIGERIAN ta ruwaito cewa gwamnatin jihar ta dakatar da Mista Rimingado ne bayan bude bincike kan wasu kwangiloli da ake zargin an baiwa wasu kamfanoni masu alaka da iyalan gwamnan. A zaman da aka ci gaba da yi a ranar Talatar da ta gabata, Bankin ta bakin lauyansa Joshua Shekwolo ya shaida wa kotun a cikin wata takardar neman sahalewa cewa gwamnatin jihar Kano ta na da asusun ajiyar banki da jimillar kudaden da suka kai N5,713,891.22 kasancewar an toshe hukuncin da aka yanke kan lamarin. a cikin asusun. Da yake bayar da cikakkiyar umarnin, mai shari’a O.O Oyewumi ya umarci GTBank ya biya kudin a asusun Mista Rimingado

Shugaba Biden ya bayyana aniyar sake tsayawa takara

Image
  Shugaban Amurka Joe Biden ya sanar da cewa zai sake tsayawa takara a zaÉ“en shekara ta 2024, inda mai yiwuwa ya sake takara da Donald Trump. An yi tsammanin jam'iyyar Democrat za ta sake neman wa'adin mulki na biyu tsawon shekara huÉ—u tare da Æ™addamar da yaÆ™in neman zaÉ“ensa a wani bidiyo ranar Talata. Ya ce wannan muhimmin lokaci ne da zai sake bayyana aniyrasa ta sake neman mulkin Amurka. Mataimakiyar shugaban Æ™asar Kamala Harris, mai shekaru 58, ita ma ta nuna aniyar sake zama abokin takararsa. Mista Biden, mai shekaru 80, shi ne shugaban Æ™asa mafi tsufa a tarihin Amurka, kuma da alama zai fuskanci tambayoyi kan shekarunsa a tsawon lokacin yakin neman zaÉ“e. Zai kasance mai shekara 86 bayan kammala wa'adinsa na biyu a mulkii cikin shekara ta 2029. BBC Article share tools

’Yan Matan Chibok’ 2 Sun Gudo Daga Hannun Boko Haram

Image
  Karin mutum biyu daga cikin daliban Makarantar Sakandaren ’Yan Mata da ke Chibok a Jihar Borno sun gudo daga hannun mayakan Boko Haram da suka sace su shekaru tara da suka gabata. Majiyoyin tsaro da mazauna Jihar Borno sun shaida wa wakilinmu cewa matan su biyu sun samu tserewa a dalilin tsananta luguden wuta da sojoji suke yi a kan sansanonin kungiyar da ke Dajin Sambisa Wata majiyar tsaro ta ce daliban da suka gudo su ne Hauwa Mutah da kuma Esther Markus. Ta bayyana cewa, “Daya daga cikinsu ’yar kauyen Chibok ce, dayar kuma ’yar kauyen Dzilang ce.” Kawo yanzu daliban makarantar 96 ne suka rage a hannun kungiyar Boko Haram da ta sace su tun a watan Afrilun shekarar 2014. Mako biyu da suka gabata, rundubar soji ta Operation Hadinkai da ke yaki da kungiyar, ta bayyana cewa akwai saura mutum 98 daga cikin Daliban Chibok a hannun kungiyar. Kwamandan Sashen Lelen Asiri na rundunar, Kanar Obinna Ezuipke ya ce, “Daga cikin Daliban Chibok 276 da aka sace, 57 sun tsere a 2014, an sako 107 a

‘Yan sanda sun fara farautar shugaban INEC na Adamawa

Image
Babban Sufeton 'yan sandan Najeriya Usman Alkali Baba ya umurci wata tawagar 'yan sanda ta yi aiki tare da hukumar zaben Najeriya INEC wajen bincike da kuma gurfanar da shugaban hukumar zabe na jihar Adamawa da aka dakatar Hudu Yunusa Ari. A wata sanarwar da rundunar ta fitar wacce kakakinta Olumuyiwa Adejobi ya sanya wa hannu, babban sufeton ya ce 'yan sanda za su tabbatar sun yi dukkan mai yiwuwa domin gano dalilin da ya sa Hudu aikata abun da ya yi. Ana tsaka da tattara sakamakon zaɓen gwamna na jihar Adamawa da aka ƙarasa ne sai kwatsam Hudu wanda shi ne kwamishinan zaɓe na jihar, ya ayyana Sanata Aishatu Binani ta APC a matsayin wadda ta lashe zaɓen. IGP Usman ya ce a shirye su ke su tabbatar an yi hukunci da ya dace kan dukkan wadanda aka samu da hannu a lamarin da ya faru a Adamawa domin martaba dokokin dimokradiya. Sanarwar ta tabbatar wa 'yan Najeriya da kuma kasashen duniya cewa 'yan sanda za su binciki ayyana Aishatu Binani ta APC da Hudun ya yi tare saur