Search This Blog

Friday, 13 January 2023

'Yan bindigar da suka yi garkuwa da ni suna so su isarwa da gwamnati wani sake ne - Kanal 'Yandoto


 

Shugaba Buhari ya gargaɗi ƙasashen ƙetare kan zaɓen Najeriya

Shugaba Muhammadu Buhari na Najeriya ya gargaɗi gwamnatocin ƙasashen ketare kan tsoma baki ko katsalanda a harkokin cikin gidan ƙasar musamman a lokutan zaɓe da ke tafe kasa da kwanaki 42.

Majiyarmu ta rawaito cewa Shugaban ya sanar da hakan ne lokacin da yake maraba da sabbin jakadun Switzerland da Sweden da Jamhuriyar Ireland da Thailand da Senegal da Sudan ta Kudu a fadar gwamnati.

Shugaban ya ce Najeriya tana aiki kafada-kafada da kungiyar ƙasashen yammacin Afirka Ecowas domin shawo kan matsalolin tsaro da bijiro da matakan tabbatar da zaɓe mai sahihanci ba tare da katsalanda ga kudin tsarin mulkin kasa ba.

Ko a shekarar da ta gabata sai dai shugaba Buhari ya yi irin wannan gargadi inda yake cewa burinsa shi ne ganin anyi sahihin zaɓe cikin kwanciyar hankali.

Abin da ya faɗawa jakadun
Wata sanarwa da kakakinsa Femi Adesina ya fitar ta rawaito shugaba Buharin ya gargadin jakadun ketare kan su mayar da hankali kan abin da ya shafesu da dalilan turo su Najeriya, da kuma kawar da kai kan abubuwan da ba huruminsu ba ne.

Buhari ya ce babu shaka dole za a sa ido kan yada zaɓukan Najeriya za su kasance don haka fatansa shi ne ganin wakilan ƙasashen sun mayar da hankali wajen shirya yada ayyukansu zai kasance domin tabbatar da ganin komai ya tafi cikin kwanciyar hankali.

Sannan ya shaida mu su cewa Najeriya tana aiki sosai da Ecowas domin tabbatar da cewa an mututun dokokin kudin tsarin mulki ba wai kowa damar ‘yanci zaɓen abin da yake so.

Ya kuma jadada cewa yana alfahari da farin ciki irin haɗin-kan da ƙasashen ke bai wa Najeriya musamman a fanonin da suka shafi tsaro da yaƙi da rashawa da inganta tattalin arziki da kuma kokarin haɓɓaka shugabanci na gari.

Ya nemi hadin-kan sauran kasashen duniya wajen shawo kan manyan kalubalen Najeriya da yammacin Afirka.


Martanin jakadun
Wakilan ƙasashen da suka gana da shugaba Buharin sun alkawarta mutunta dokoki da taimakawa Najeriya wajen kare muradanta da kuma tabbatar da ganin an yi zaɓe cikin sahihanci.

Sun ce suna sanne da matsayin Najeriya a Afirka baki ɗaya, da matsayarta a siyasar duniya da girman tattalin arzikinta.

Jakadun sun yi wa kasar fatan alheri wajen ganin an yi zaɓen 2023 cikin kwanciyar hankali da cikakken tsaro.

Kwanaki 42 suka saura 'yan Najeriya su fita rumfunan zabe domin kada kuri'unsu a zaben shugaban kasa.

Duk da cewa an dan bayyana fargabar wasu matsaloli da ka iya yiwa zaben tarnaki ko haifar da tsaiko, shugaba Buhari ya jadadda cewa zabukan za su gudana kamar yada aka tsara.

Sannan ita ma hukumar zabe ta yi watsi da raɗe-raɗin da wasu bayanai da aka rinka yaɗawa kan yiwuwar dage zaɓen.

'Yan Najeriya dai yanzu hankali ya karkata domin ganin yada za ta kaya a babban zaɓen da ke shirin riskarsu cikin yanayi na matsin tattalin arziki da matsalolin tsaro



Gwamna Ganduje ya bayyana Dr. Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin Mutum mai Biyayya da Amana

Dr. Abdullahi Umar Ganduje ya bayyana hakan a yayin taron yakin neman zaben jam'iyyar APC a kananan hukumomin Sumaila da Takai.

Ya kuma bukaci al’ummar kananan hukumomin biyu da su zabi dan takarar gwamna na jam’iyyar APC da abokin takararsa domin dukkansu an gwada su kuma an amince da su.

Gwamnan ya bayyana cewa su biyun sun cancanci a zabe su saboda irin nasarorin da suka samu a ma’aikatun gwamnati daban-daban da suka yi aiki a tsawon shekaru.

Dakta Ganduje ya yi nuni da cewa Dr. Nasiru Yusuf Gawauna da Alhaji Murtala Garo sun cancanta haka kuma su sukafi da cewa su gajeshi domin ci gaba da ayyuka da shirye-shiryen gwamnati a bangarori daban-daban da Gina dan Adam.

Ya kuma bayyana fatansa na cewa ‘yan takarar na da kwarewa wajen fito da manufofi da shirye shirye da kuma aiwatar da karin manufofi da tsare-tsare da suka shafi ci gaban jihar, idan har aka ba su wa’adi a babban zabe mai zuwa.

Gwamnan ya yi amfani da damar wajen yin kira ga masu zabe da su kada kuri’ar su ga dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar Sanata Asiwaju Bola Ahmad Tinubu inda ya bayyana shi a matsayin mutum mai rikon amana, mai dattako da kwarewa don kai Najeriya mataki na gaba.

A nasa bangaren mataimakin gwamnan jihar wanda kuma shi ne dan takarar gwamna na jam’iyyar APC Dr Nasiru Yusuf Gawauna, ya bayyana cewa daga dukkan alamu za a zabi shi da abokin takararsa a matsayin gwamna da mataimakin gwamna idan Allah ya yarda.

Ya kuma yi kira ga al’ummar yankin da su zabi jam’iyya mai mulki a lokacin zaben Gwamna da ke karatiwa, inda ya yi alkawarin aiwatar da kuduririn da ya alkarwanta.

Tun da farko, shugaban jam’iyyar APC na jiha Alhaji Abdullahi Abbas, ya ce yawan jama’ar da suka halarci taron gangamin yakin Neman zaben shaida ce a fili cewa jam’iyyar APC ce za ta lashe dukkan mukamai a zabe mai zuwa.

Daga cikin abubuwan da aka gudanar a wajen taron ya hada da mika tutar jam'iyyar APC ga Dan takarar majalisar wakilai ta tarayya da na majalisar dokokin jiha na yankin.

Zan mayar da Wa'adin Sakamakon JAMB Shekara 4 - Sanata Kwankwaso

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar NNPP Rabiu Musa Kwankwaso yayi alkawarin tsawaita wa’adin sakamakon jarabawar shiga jami’a (JAMB) zuwa shekaru hudu idan ya ci zaben shugaban kasa.

Majiyarmu ta rawaito cewa Kwankwaso ya bayyana hakan ne a Bauchi, lokacin da yake mika tutoci ga ’yan takarar gwamna shida da na Majalisar Dattijai 18 na yankin Arewa maso Gabashin Najeriya ranar Alhamis.

An yi garkuwa da DPO a Filato
Yadda aka yi wa Sakkwatawa kisan gilla a Anambra
Kwankwaso ya ce dalibai da dama na samun sakamako mai kyau a rubuta jarabawar karo na farko, amma da zarar sun rasa gurbi a jami’a sai sun sake sabon lale bayan ba laifinsu ba ne.

“Babu gaira babu dalili an sanya daliban da iyayensu lalubo kudin zana jarrabawa na shekaru biyu koma fiye. Haka ne ya sanya muku ga dacewar sauya haka.


“Haka kuma za mu kirkiri sabuwar dokar dakatar da jarabawar JAMB din na tsawon shekaru hudu, domin ’ya’yanmu su yi amfani da sakamakon wajen samun gurbin karatu a manyan makarantun a wannan tsakanin,” inji shi.

Dan takarar shugaban kasar ya kuma yi alkawarin maida bada fom din neman gurbi a jami’o’i, da na neman aiki kyauta matukar aka zabe shi a matsayin shugaban kasar Najeriya.

Duk wanda ya yake ni Sai ya gane kurensa - Kwankwaso

Dan karar shugaban kasa na Jam’iar NNPP, Sana Rabiu Musa Kwankwaso, ya ce duk wanda ya yake shi a Jihar Kano a zaben 2023, sai ya yaba wa aya zaki.

Jaridar Aminiya ta rawaito cewa Kalaman tsohon gwamnan jihar na zuwa ne bayan gwamna mai ci kuma wanda ba sa ga maciji, Abdullahi Ganduje, ya ce wa magoya bayan Jam’iyyar APC, a 2023 Kano za ta maimaita abin da ta yi a zaben shugaban kasa na shekarar 1993.


Ana ganin kalaman na Ganduje tamkar gugar zana ce cewa Kananawa ba za su zabi Kwankwaso ba a zaben da ke tafe a ranar 25 ga waan Fabrairu.

Amma a martanin Kwankwaso, ya ce, “Ba na son kula wancan mutumin, ban san ko ya fada ko bai fada ba, amma duk wanda ya yaki NNPP ko Kwankwaso a 2023 sai ya i da-na-sani.”


Ya ci gaba da cewa, “Duk wanda ya san ni, ya san abin da na yi a baya, ya san idan na ci zaben shugabna kasa, Kano za ta fi kowa amfana, Arewa za ta amfana, haka kuma kasa baki daya.”

A cewarsa, “Kwanan nan yi gangamin yakin neman zabe wadanda ke cikin mafiya kayatarwa, ba irin na wasu ’an takara da baki daga wasu jihohi suka shigo ba — Na yi daya a Wudil, Kudancin Kano, daya a Bichi, Arewacin Kano; sannan na bude ofishin yakin neman zabe a Kano ta tsakiya.

“Abin mamaki shi ne wai ni za a ce in kira gangamin yakin neman zabe a Kano; Sau nawa kuma; ko a kwananan daga watan Disamba zuwa Janairun nan na yi; don haka mene ne kaya gabas don ka yi akin neman zabe a Kano?”

Najeriya Ta Rattaba Hannu Kan Yarjejeniyar Gudanar Da Aikin Hajjin Bana Da Saudiyya



 Najeriya ta samu nasarar yin taro da hukumomin aikin hajji na Saudiyya, inda aka sanya hannu kan yarjejeniyar gudanar da aikin hajjin bana.

Karamin ministan wajen Najeriya Ambasada Zubairu Dada ne ya jagoranci tawagar Najeriya wajen kulla wannan yarjejeniya da ke zama ka’idar amincewa kowace kasa ta kawo alhazai.

Rattaba hannu kan yarjejeniyar ya biyo bayan wata ganawa ta yanar gizo tsakanin shugaban hukumar Alhazan Zikrullah Kunle Hassan da hukumomin aikin hajji na Saudiyya a watan Disambar bara.

Kwamishinan ma’aikata da tsara manufofi na hukumar Alhazan Nura Hassan Yakasai wanda ke cikin tawagar ya bayyana cewa Saudiyya ta amince da dawowa da Najeriya yawan kujeru na asali da ta ke samu mutum dubu 95.




Hakanan Yakasai ya ce a yanzu ba dogon bincike kan cutar korona bairos matukar maniyyaci ya na da shaidar gwajin cutar.

Malamai sun shiga fadakar da maniyyata don kara fahimtar dokokin aikin da zummar samun ladan wankuwa daga zanubai.

Shugaban JIBWIS Sheikh Abdullahi Bala Lau ya bukaci kara karfafa koyar da maniyyatan aikin daga Najeriya har zuwa Makkah da Madina.


A shekarun baya ‘yan Najeriya kan saye dukkan kujerun aikin hajji har ma a saura da bukatar masu son zuwa, amma gabanin bullar annoba an samu kujerun da su ka yi kwantai don rashin karfin arzikin jama’a ko wadatar abun hannu da ya kara ta’azzara daga rage daukar nauyin lamuran hajji da gwamnatoci su ka yi.

Sabbin Katinan Zabe 13m Muka Buga —INEC


Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) na bincike kan zargin jami’anta da karbar na goro a aikin rabon katin zabe da ke gudana.

Hukumar ta kara da cewa ta buga sabbin katinan zabe miliyan 13 da dubu 868 da 441 bayan kammala aikin rajistar sabbin masu zabe.

Da yake sanar da hakan, Kwamishinan INEC na Kasa kan Wayar da Masu Zabe da Yada Labarai, Festus Okoye, ya ce, “Hukumar ta damu bayan samun korafe-korafe kan nuna fifiko a wasu wuraren rabon katin.

“Duk halastattun masu rajista na da ’yancin karbar katinsu domin kada kuri’a a ranar zabe a wuraren da suka yi rajista.”

“Domin kawar da shakku, sabbin katunan zabe miliyan 3 da dubu 868 da 441 INEC ta buga da suka hada da na sabbin wadanda suka yi rajista da wadanda suka sauya wurin zabe da kuma wadanda aka sabunta katinsu.”

Okoye ya sanar cewa hukumar ta kara lokacin rabon katin zuwa ranar 29 ga watan Janairu da muke ciki, daga karfe 9 na safe zuwa 3 na rana, har da ranakun Asabar da Lahadi.

Hukumar ta kuma umarci jami’anta masu aikin rabon katin da su tattara duk wani korafi rashin buga kati zuwa ga shugabanninsu a jihohi domin daukar matakin da ya dace.

(AMINIYA)

Hari Kan NSCDC: Kar Ku Raga Wa ’Yan Bindiga —Buhari Ga Sojoji


 Shugaba Buhari ya yi Allah wadai da kisan jami’an Sibil Difens bakwai da wasu ’yan bindiga suka yi a Kaduna.

Cikin wata sanarwa da kakakinsa Garba Shehu ya fitar ranar Alhamis, Buharin ya bayyana takaicinsa da kisan jajirtattun jami’an da ya ce sun sadaukar da rayuwarsu ga Najeriya.

“Jami’an NSCDC din da suka sadaukar da rayuwarsu wajen tsare kasarmu ba karamin jihadi suka yi ba a bakin aikinsu.

“Ina jajanta wa iyalai da ’yan uwa da abikan arzikinsu. Ina rokon Ubangiji Ya ba su ikon jure wannan rashi”, in ji Buhari.

Daga nan ne kuma shugaban ya umarci rundunar sojojin Najeriya da su kamo ’yan bindigar su yi maganinsu.

Thursday, 12 January 2023

Mutum 26 Sun Saye Kadarorin Diezani Da Aka Yi Gwanjonsu


Akalla mutum 26 ne suka saye kadarorin da gwamnati ta yi gwanjonsu bayan kwato su daga hannun barayin gwamnati.

Kadarorin sun hada da gidaje da filaye da aka kwato daga tsohuwar Ministar Man Fetur, Diezani Allison-Madueke, a Abuja da sauran wurare.

A shekarar da ta gabata Hukumar Yaki da Rashawa (EFCC) ta yi gwanjon kadarorin ga masu son sayen su.

Jaridar Aminiya ta rawaito cewa, a ranar Litinin hukumar ta fara mika kadarorin da aka saye na Legas da Abuja da Fatakwal da Kano da sauran wurare.

Sai dai kadarorin sun yi kwantai a ranar Liinin da aka yi gwanjon su, ko mutum guda ba a samu da ya sayi ko da daya daga cikinsu ba.

Amma mutum shida daga cikin 90 da suka nema suka yi nasara a rukuni na hudu a ranar Talata.

Da yake sanar da wadanda suka yi nasara a ranar Alhamis, mai magana da yawun EFCC, Wilson Uwujaren, ya ce kadarori 26 sun samu shiga, 13 kuma sun gaza, saboda rashin cika ka’ida da sauransu.

A cewar Uwujaren, “Kadarori 39 ne a rukuni na biyar wadanda ke a wurare daban-daban a cikin Abuja.”


A cewar Uwujaren, “Kadarori 39 ne a rukuni na biyar wadanda ke a wurare daban-daban a cikin Abuja.”
Ya ce za a sake bude kofa don bai wa mabukata su sayi kadarorin da suka rage a rukuni na biyar.

Da yake jawabi tun da farko, Shugaban EFCC, Abdulrasheed Bawa, wanda a gabansa komai ya gudana ya ce, hukumar ta yi aiki tare da masana harkokin gidaje don tabbatar da ba a sayar da wata kadara kasa da darajarta ba.

“Yadda muka tafiyar da tasarin haka lamarin yake a kasashen duniya.

“Muna da masana kadarori da suka tantance mana darajar kowace kadara, kuma muna sa ran sallama wa wanda ya biya fiye da saura.

“Saboda muna da bukatar tara wa Gwamnatin Tarayya kudi don aiwatar da sabbi da kammala wasu manyan ayyukan da ke gabanta a sassan kasa.

“Mun samu korafe-korafen jama’a kan dalilin rashin gudanar da shirin ta intanet. Mun jarraba haka, amma sai muka zabi tsarin da zai ba mu damar yin komai a bayyane don ’yan kasa su shaida,” in ji Bawa.

Daya daga cikin wadanda suka samu nasarar mai suna Chetanna Chukwudo, ya bayyana jin dadinsa tare da kira ga EFCC da ta ci gaba da kyakkyawan aikin da ta sa gaba saboda ’yan kasa na tsumayar kyakkyawan cigaba daga gare ta.

LABARI DA DUMIDUMINSA! INEC ta kara wa’adin lokacin Karbar katin zabe

Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta kara wa’adin da ta sanar na kammala rabon katin zabe da mako guda a fadin Najeriya.

Karin bayani na tafe

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Presidential delegation pays condolence visit to Hamza Darma’s family in Kano

A high-powered presidential delegation has paid a condolence visit to the family of late Alhaji Hamza Usman Darma, a prominent K...