Search This Blog

Tuesday, 10 January 2023

Maharan Jirgin Edo Na Neman Fansar N520m

Yan bindigar da suka sace fasinjoji a Tashar Jirgin kasa ta Ekehen da ke Jihar Edo na neman Naira miliyan 520 a matsayin kudin fansa.

Rahotanni sun ce maharan sun kira iyalan fasinjoji 26 da ke hannunsu, suka yanka musu fansar Naira miliyan 20 a kan duk mutum daya.

Zan dora daga inda El-Rufai ya tsaya a Kaduna —Uba Sani
Kano 2023: Dalilin ba wa Gawuna takarar Gwamna —Ganduje
Wani shugaban matasa a yankin, Benson Ordia, da ya tabbatar da hakan, ya ce gwamnatin jihar ta ce za ta gudanar da bincike na tsanaki a yankin.

Sai dai kakakin ’yan sandan jihar, Chidi Nwanbuzor, ya ce ba shi da masaniya kan kudin fansar da maharan suka yanke kan fasinjojin.


A ranar Asabar ce maharan suka kai hari tare da yin awon gaba da fasinjoji akalla 32 a tashar jirgin kasan.

Sai dai jami’an tsaro sun ceto mutum shida daga cikin fasinjojin jirgin kasan da aka sace, wadanda uku daga cikinsu kananan yara ne.

Wannan dai shi ne karo na biyu da ’yan bindiga ke kai wa jirgin kasa hari tare da sace fasinjoji, bayan wani hari da suka kai wa jirgin kasan Abuja zuwa Kaduna a watan Maris din 2022

Na Cika Alkawuran Da Na Daukar Wa ’Yan Najeriya – Buhari

Shugaban Najeriya, Muhammadu Buhari, ya ce ya cika alkawuran da ya dauka na yaki da ’yan ta’addan boko Haram da farfado da tattalin arziki da kuma yaki da cin hanci da rashawa.

A cewar Kakakin Shugaban, Femi Adesina, Buhari ya bayyana hakan ne yayin wanin taron cin abinci da aka shirya domin karrama shi a Damaturu, babban birnin jihar Yobe.

Giwa ta kashe manomi a Uganda
’Yan bindiga sun harbe jami’an tsaro 12 a Kaduna
Shugaban dai ya fara ziyarar yinin biyu ne a Jihar ranar Litinin.

Sanarwar ta kuma ce Shugaban ya bigi kirjin cewa babu wanda zai zarge shi da tara dukiyar da ba ta halas ba lokacin da yake mulki, inda ya ce ko taku daya ba shi da shi a wajen Najeriya.
A wani labarin kuma, Shugaban ya ce babu wata kungiyar ’yan ta’adda da ta isa ta wargaza Najeriya.

Shugaban Kasar ya bayyana haka ne yayin da ya kai ziyara fadar Sarkin Damaturu, Alhaji Hashumi Ibn Elkanemi II a fadarsa da ke garin Damaturu, ranar Talata.

Buhari ya kuma bukaci ’yan Najeriya da su kara kaimi tare da ba da karfin gwiwa ga hukumomin tsaro kan kokarinsu na zaman Najeriya kasa daya dunkulalliya.

“A watanni hudu masu zuwa, in na bar mukamin Shugaban Kasa, zan ci gaba ne da dagewa, kuma ina fatan zan aiki lafiya.”

“Dole ne mu samar da kwarin gwiwa a kasarmu tare da tabbatar da cewa ba mu kawo cikas ga tsaro ba ta kowace fuska domin tsaro da tattalin arziki su ne mafi muhimmanci ga kowace kasa.

“Mun sha fama da yawa wajen hada kan kasar nan, kuma ina rokon ku da ku dage da tabbatar da cewa ba za mu bari wani ya sake wargaza mu ba,” in ji shi.

Shugaban ya kuma bayyana farin cikinsa da dawowar zaman lafiya da kwanciyar hankali a jihar Yobe da ma yankin Arewa maso Gabashin Najeriya, inda ya gode wa Gwamnan Yobe, Mai Mala Buni da takwaransa na jihar Borno, Farfesa Babagana Zulum, bisa jajircewar da suka yi na sake gina makarantu, cibiyoyin lafiya da cibiyoyin da ’yan ta’addan suka lalata.

Shugaban ya ce, ya lura da cewa ‘’da gangan aka yi yunkurin ruguza Najeriya amma Allah bai yarda ba,’’ ya kara da cewa ‘’Allah ya taimaki Najeriya ta dawo.

Ya kuma yabawa jami’an soji da ‘yan sanda bisa sadaukarwar da suke yi wajen kare Kasar nan daga fadawa cikin mummuna yanayi.

Shugaban ya kara da cewa, da suka yi yaki don kare hadin kan Najeriya a lokacin yakin basasa, wadanda ke cikin wannan kwarewa ba za su taba barin wani ya sake ruguza kasar nan ba

Da ya ke jawabi, Gwamna Buni ya shaida wa Shugaban Kasar cewa, a cikin wannan yakin da ake yi da ’yan tada kayar baya, ’yan ta’adda sun taba mamaye hatta fadar Sarkin Damaturu a baya.

Sai dai ya ce tun bayan zuwan gwamnatin APC a 2015, Jihar ta samu sa’ida.

Shi kuwa Sarkin na Damaturu ya mika godiyarsa ga Shugaban Kasar kan inganta harkokin tsaro a kasar, inda ya ce, “Mun sha wahala a baya, amma gwamnatinka ta hada kan kasa cikin ikon Allah.”
(AMINIYA) 

Monday, 9 January 2023

Kuyi amfani da kalaman da al'uma zasu gamu dasu wajan yakin neman zabe: Mai Martaba Sarkin Kano.

Mai martaba sarkin kano Alhaji Aminu Ad Bayero ya yi kira ga masu neman kujerun mulkin kasar nan da su tabbatar sunyi kalamai da al'umma za su gamsu da su wajen neman kuri'ar alumma a zaben shekarar 2023.

A sanarwar da Sakataren yada labaran Masarautar Abubakar Balarabe Kofar Naisa ya sanyawa hannu, ta ce Sarkin ya bayyana haka ne lokaci da dan takarar shugaban kasa na jam'iyar SDP Adewale Adebayo da dantakar kujerar gwamnan jihar Kano Dr. Muhammad Bala gwagwarwa yayin da su ka  ziyar ce shi a fadar sa.

Alhaji Aminu Bayero, ya kuma nemi da duk wani dake neman kujerar da yasan cewa Allah ne ke bayar da Mulki bawai karfin ikon tada zaune tsayeba.

Da yake nasa jawabin, dan takarar Gwamna na jam'iyyar ta SDP Bala Muhammad Gwagwarwa ya ce sun ziyarci fadar sarkin ne domin neman tabaraki da addu'ar.

A wani cigaban kuma Martaba Sarkin kano Alhaji Aminu Ado Bayero ya nada Dr. Malam Umar Ibrahim Indabawa  a matsayin sabon limamin  Masallacin Darul hadis dake Unguwar Tudun Yola a Karamar  Hukumar Gwale.


Ni Na Dora Bala A Gwamna, Kuma Ni Zan Sauke Shi – Tsohon Wazirin Bauchi

 


Tubabben Wazirin Bauchi, Muhammadu Bello Kirfi, ya sha alwashin sai ya cire Gwamnan Jihar, Bala Mohammed, daga mukaminsa kamar yadda shi ma ya cire shi daga mukaminsa.

Kirfi ya bayyana haka ne sakamakon tube masa rawani da Masarautar Bauchi ta yi masa a matsayin Wazirin Bauchi.

Masarautar Bauchi ta tube tsohon Wazirin ne saboda abin da ta kira da rashin biyayya ga Gwamnan Jihar.

Da yake zantawa da manema labarai ranar Lahadi, Kirfi ya ce, “Hanyar da na shigar da shi ofis, ta nan zai bi ya fita.

“Ina daya daga cikin wadanda suka tsaya masa ya samu Gwamna, kuma na ji takaicin abin.

“Wannan shi ne iya abin da zai iya yi, ba komai ba ne wannan saboda babu wata riba da nake samu (a matsayin Waziri) a Fadar Sarki.”

Kazalika, Kirfi ya ce Gwamnan ya ci amanar jiga-jigan ‘yan siyasar da suka taimaka masa wajen cin zabe.

Ya ce Bala ya yi fada da kusan baki dayan wadanda suka yi ruwa da tsaki a zaben da ya lashe 2019.

“Na bar wa Allah komai, Shi ne zai yi mana shari’a kan abin da ke tsakanina da shi,” in ji shi.

A wajen jama’ar Bauchi Gwamna Mohammed ke neman a sake zabensa amma ba a wajen mutum guda ba saboda Allah ke ba da mulki ga wanda ya so,” in ji Zainabari

Akwai Yiwuwar Matsalar Tsaro Ta Kawo Wa Zaben 2023 Tangarda – INEC



Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) ta yi gargadin cewa matsalar tsaron da ake fama da ita a wasu sassan Najeriya za ta iya sa wa a soke babban zaben 2023 da za a fara a watan gobe.

Shugaban hukumar, Farfesa Mahmud Yakubu, wanda Shugaban Cibiyar Bincike Kan



Harkokin Zabe (BEI), Farfesa Abdullahi Abdu Zuru ya wakilta ne ya yi gargadin ranar Litinin a Abuja.

Ya bayyana hakan ne yayin wani taron ba da horo kan shirye-shiryen tsaro a lokacin zaben.

Hukumar ta ce matsalar na iya sa wa a gaza gudanar da zaben a mazabu da dama, ta yadda zai yi wahala a iya bayyana wanda ya lashe shi, wanda ta ce hakan zai haifar da rudani a tsarin mulkin Najeriya.

Zan tattauna da masu tayar da kayar baya idan na zama shugaban kasa - Peter Obi

Ɗan takarar gwamna a Jam'iyyar Labour a Najeriya Peter Obi ya ce zai buƙaci ya tattauna da duk wani ɗan gwagwarmaya ko kuma masu tayar da ƙayar baya da gwamnatin Najeriya ta ɗaure idan ya samu mulkin ƙasar.

Mista Obi ya bayyana haka ne a wani zauren tattaunawa da tambayoyi da gidan talabijin na Channels a Najeriya ya shirya ga ɗan takarar da mataimakinsa.

Ko da wani ya tambayi Mista Obi ko cikin waɗanda zai tattauna da su har da ƴan Boko Haram da ke jawo matsaloli a arewacin Najeriya da kuma ƴan ƙungiyar IPOB da ke kudu maso gabashin ƙasar, sai ya ce " Zan tattauna da dukansu, ko ma wace irin bindiga ce suke ɗauke da ita".

Mista Obi ya ce ko da mutum yana ɗaure a gidan yari ne zai je ya fito da shi domin su zauna su tattauna.


Mista Obi ya ce ya yanke hukuncin yin haka ne domin ganin cewa an samu zaman lafiya a ƙasar.

"Zan tattauna da waɗanda suke so a tattauna da su. Sai an kalli me ke jawo suke gwagwarmaya; batu ne na rashin adalci ko lamari ne na talauci ko rashin aikin yi," in ji Mista Obi.

Mista Obi ya bayyana cewa idan gwamnati ta soma mayar da hankali kan batun zama da tattaunawa da ƴan ƙasar, babu wani ɗan gwagwarmaya a duniya da zai samu wani dalili na tayar da zaune tsaye sakamakon duk wata buƙata an biya ta.

Najeriya dai ta sha fama da zanga-zanga ta masu son ɓallewa daga ƙasar kamar ƙungiyar IPOB masu iƙirarin kafa ƙasar Biafra.

Yanzu haka jagoran ƙungiyar Nnamdi Kanu na ci gaba da zama a tsare a hannun jami'an tsaron Najeriya kan wasu zarge-zarge ciki har da na ta'addanci
(BBC HAUSA) 

An kori Farfesa daga aiki saboda nuna zanen hoton Annabi lokacin koyarwa

Jami’ar Hamline da ke birnin Minnesota na Amurka, ta kori wata Farfesa, Erika López-Prater, saboda nuna zanen Annabi Muhammad (S.A.W) yayin da take koyarwa.

A cewar rahotanni, wata daliba ce a ajin da take koyarwar ta yi korafi ga hukumar jami’ar.

An yi garkuwa da tsohon dan Majalisa a Edo
Isra’ila ta ba da umarnin cire tutocin Falasdinu daga gine-ginen gwamnati
Dalibar, mai suna Aram Wedatalla, ta shaida wa jaridar makarantar cewa ranta ya yi matukar baci da abin da malamar ta yi.

Aram dai wacce ’yar asalin kasar Sudan ce ta kuma ce ba za ta taba yarda ta zauna a cikin duk al’ummar da ba za ta mutunta abubuwan da ta yi amanna da su ba.


“A matsayina na Musulma kuma bakar fata, bana tunanin zan taba sakin jiki da kowacce irin al’ummar da ba ta mutunta ni kamar yadda nake mutunta ta,” inji ta.

Jaridar New York Times ta Amurka ta rawaito cewa Farfesar mai shekara 42, ta yi katobarar ce yayin wani ajin da take koyar da Tarihi, kodayake ta ce ta yi matukar taka-tsatsan kafin nuna zanen ga daliban.

Sai dai ta ce tun gabanin fara koyar da darasin, ta sanar da cewa za ta nuna hotunan Annabawa da sauran abubuwa masu tsarki, ciki har da na Musulmai da na addinin Buddha, kuma ta tambayi duk mai korafi a kai ya sanar da ita, amma babu dalibin da ya yi hakan.

Farfesar ta kuma ce ko a ajin ma, sai da ta sanar cewa za ta nuna hotunan na wasu ’yan mintuna, ko da wani daga cikin daliban na son ficewa saboda kada ya gani.


Sai dai malamar ta yi ikirarin cewa ba ta nuna hotunan domin cin zarafin Musulunci ba, inda ta ce hatta hotonta sai da ta nuna a lokacin da take dalibar jami’a a cikin ajin.



2023: Dalilin Da Ya Sa Muka Tsayar Da Gawuna Takarar Gwamnan Kano– Ganduje

 


Gwamnan Jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje, ya ce masu ruwa da tsaki na jam’iyyar APC a jihar sun tsayar da Mataimakinsa, Nasiru Yusuf Gawuna, a matsayin dan takarar Gwamnan jam’iyyar a zaben 2023 ne saboda kwarewarsa.

Ya ce biyayya da ilimi da kwarewa da kuma kyakkyawar mu’amalarsa da jama’a su ne suka karfafa zaben nasa.

Yana mai cewa, babu wata jam’iyya a Kano da ke da dan takara kwararre irin Gawuna.

Ganduje ya bayyana haka ne a lokacin da yake jawabi a wajen taron gidauniyar da abokin Gawuna ya shirya a Abuja.

“Dokta Gawuna na sane da shirye-shirye da kuma ayyukanmu, kuma mun yi amannar mutum ne wanda zai taimaka wa cigaban al’uma.

“Wannan shi ne irin mutanen da muke raino, wadanda za su yi tsayin daka wajen ci gaba daga inda aka tsaya da kyawawan ayyukan bunkasa al’uma da aka asassa. Inshaa Allah za mu ci gaba da haka.

A cewar Ganduje, “Daya daga cikin abubuwan da muka yi la’akri da su shi ne ci gaba da ayyuka saboda muhimmancin hakan a sha’anin shugabannci.

“Mun tattara bayanan cigaban da muke bukata, kuma muddin aka rasa ci gaba wajen aiwatarwa abubuwa za su watse, ba za mu kai ko’ina ba.”

“Shi ya sa bayan ya tafi ban bukaci sai wani ya fada mini ayyukan da zan aiwatar ba saboda na san komai, kuma ba ni da dalilin yin watsi da su,” in ji shi.

A nasa bangaren, Gawuna ya ce ci gaba daga inda gwamnatin baya ta tsaya shi ne sirrin samun kyakkywan sakamako.

Ya kara da cewa, “Kwarewata na da muhimmanci, kuma a shirye nake in yi amfani da ilimin da na koya na shekaru wajen yi wa jiharmu hidima.”

(AMINIYA)

Za a haramta amfani da cokali da farantin soso a Ingila

...

Gwamnmati a Ingila ta tabbatar da cewa za ta haramta kayan cin abinci waɗanda ake amfani da su sau ɗaya ana jefarwa, kamar cokali da farantan soso.

Ba a san yaushe ne harmacin zai fara aiki ba, amma hakan na zuwa ne bayan irin wannan yunƙuri a yankunan Wales da Scotland.

Sakatariya mai kula da harkar muhalli, Therese Coffey ta ce za a yi hakan ne saboda a kare muhalli domin amfanin al'ummar da za ta zo nan gaba.

Masu hanƙoro sun yi maraba da shirin, sai dai sun buƙaci a ɓullo da ƙarin hanyoyin rage amfani da robobi

Alƙaluma sun nuna cewa a ƙasar ta Ingila kowane mutum na amfani da aƙalla farantin cin abinci na roba guda 18 da kuma cokula da wuƙaƙen cin abinci 37 a kowace shekara, inda kashi 10% na irin waɗannan robobi ne kawai ake sake sarrafa su.

Sabon rikici ya kunno kai a Jam'iyar PDP reshen Jahar Kano

Wutar rikici ta ƙara ruruwa a PDPn jihar Kano duk da hukuncin kotu na baya-bayan nan da kuma matakin ɗaukaka ƙara daga ɗaya banagaren.

Lamarin ya faru ne bayan ɓangen Sadiq Wali wanda wata kotun tarayya ta ce ba shi ne ɗan takarar gwamnan ba, kuma ya ɗaukaka ƙara, daga baya ya ƙaddamar da kwamitin yaƙin neman zaɓensa a jihar.

Sai dai ɓangaren da kotu ta ce shi halastacce na Muhammad Abacha ya fito ya yi Alla-wadai da wannan mataki yana cewa nuna raini ne ga kotu.

Bayanan da BBC ta samu na cewa a wannan Litinin ɗin ne ake sa ran kwamitin yaƙin neman zaben da ɓangaren Sadiq Wali suka ƙaddamar zai fara zama domin tattauna yadda zai gudanar da aikinsa.

A makon jiya ne aka kafa kwamitin, al’amarin da ya ƙara tayar da kura.

Ɓangaren Muhammad Abacha sun ce ba su tare da wannan matakin kamar, yadda Barrister Ibrahim Isa Wangida, lauyan jam’iyyar PDP a Kano ya shaida wa BBC.

To sai dai bangaren Sadiq Wali wanda ya ƙaddamar da kwamtin ya ce, waɗanda suke sukar wannan matakin ba su fahimci yadda tsarin yake ba, a ta-bakin kakinsu Dakta Yusuf Bello Danbatta.

Masharhanta dai na ganin duk wannan rikici da taƙaddama, jam’iyyar ce ke yi wa kanta sakiyar da babu ruwa, dai-dai lokacin da hankulan sauran jam'iyyu suka karkata ga yaƙin neman zaɓe.

Jam'iyyar ta PDP da ke sahun manyan masu hamayya a Kano har yanzu kanta a rarrabe yake lamarin da ake ganin hakan ba zai yi mata kyau, kasa da wata biyu a gudanar da zabe.


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Presidential delegation pays condolence visit to Hamza Darma’s family in Kano

A high-powered presidential delegation has paid a condolence visit to the family of late Alhaji Hamza Usman Darma, a prominent K...