Yanzu-Yanzu: Shugaba Bola Ahmed Tinubu Ya Nada Sababbin Shugabannin Hukumar NAHCON

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya amince da nadin sababbin 'yan hukumar gudanarwa na hukumar alhazai ta kasa (NAHCON), har sai majalisar dattawan Najeriya ta tabbatar da hakan.


A sanarwar da mai taimakwa Shugaban kasar kan harkokin kafafen yada labarai, Ajuri Ngelale ya sanyawa hannu, yace Shugaban a cikin kudurinsa na tabbatar da gudanar da aikin Hajji na shekarar 2024 ba tare da matsala ba, ya nada wadannan mutane a Hukumar NAHCON:

Jalal Arabi - Shgaba 

Aliu Abdulrazaq - Kwamishinan tsare-tsare, Ma'aikata, da Harkokin Kudi

Prince Anofi Elegushi - Kwamishinan Ayyuka

Professor Abubakar A. Yagawal - Kwamishinan Tsare-tsare & Bincike

Wakilan shiyya: 

Dr. Muhammad Umaru Ndagi — Arewa ta tsakiya

Abba Jato Kala — Arewa maso gabas 

Sheikh Muhammad Bin Othman - Arewa maso Yamma

Tajudeen Oladejo Abefe - Kudu maso Yamma

Aishat Obi Ahmed — Kudu maso Gabas

Zainab Musa – South South

Professor Musa Inuwa Fodio — Jama’atul Nasril Islam

Farfesa Adedimiji Mahfouz Adebola — Majalisar Koli kan Harkokin Musulunci

Shugaban ya umurci wadanda aka nada su sadaukar da kansu wajen ganin cewa ayyukan hukumar alhazai ta kasa sun kasance masu inganci da gaskiya da kuma biyan bukatun ‘yan Najeriya.


Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki