Darakta Janar Na Hukumar Alhazan Kano Ya Dawo Najeriya Bayan Ziyarar Aiki Da Ya Kai Saudia

A yau ne Darakta Janar na Hukumar Jin Dadin Alhazai ta Jihar Kano, Alhaji Laminu Rabi’u Danbappa ya dawo daga kasar Saudiyya tare da tawagar magoya bayansa.

A sanarwar da Jami'in hulda da jama'a na hukumar, Sulaiman Abdullahi Dederi ya sanyawa hannu, yace da yake jawabi ga mazauna unguwar Galadanci da ke karamar hukumar Gwale da jami’an hukumar alhazai na kananan hukumomi 44, Alhaji Laminu Rabi’u ya bayyana abubuwan da ya sa a gaba a tafiyar.
 Ya mayar da hankali ne kan inganta masaukan alhazai da ciyar dasu, da sufuri ga alhazai a yayin aikin Hajjin 2024 mai zuwa.

A yayin jawabin, Alhaji Laminu Danbappa ya yi amfani da damar wajen taya Gwamnan Jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusif murnar nasarar da ya samu a kotun koli a kwanakin baya.
Ya bukaci daukacin ma’aikatan hukumar da su ba da hadin kan da ya dace domin cimma burin da aka sanya a gaba. 

Alhaji Laminu Rabi'u ya yi alkawarin yin aiki tare da dukkan ma'aikata domin cimma manufofin da aka sanya a gaba 

Ya Kuma nuna jin dadinsa, ya yabawa Gwamna Alhaji Abba Kabir Yusif bisa yadda yake ba hukumar damammaki a kai a kai.




Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki