Search This Blog
Thursday, 8 February 2024
Tsadar Kayan Abinci: Hukumar Yaki Da Cin Hanci Ta Kano Za Ta Fara Kama Dukkanin Wadanda Ta Samu Suna Boye Kayan Abinci
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Tuesday, 6 February 2024
Jahar Kano Za Ta Hada Gwiwa Da Canada A Fannonin Bunkasa Lafiya, Ilimi, Noma.
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Monday, 5 February 2024
Tsadar Rayuwa: Gwamna Abba Kabir Yusuf Ya Gana Da 'Yan Kasuwar Kano
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Sunday, 4 February 2024
Hukumar Alhazai Ta Kano Ta Sanar Da Kudin Aikin Hajjin Bana
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Hanyoyi huɗu da Facebook ya sauya duniya
Dubi hoton da ke sama. Wannan shi ne yadda Facebook, ko kuma The Facebook kamar yadda aka sani a lokacin, ya ke lokacin da Mark Zuckerberg da wasu aminansa suka ƙaddamar da shi daga matsuguninsu na dalibai shekara 20 da suka gabata.
Tun daga wannan lokacin, shahararren shafin sada zumuntar na duniya ya sake fasali da yawa.
Amma manufarsa ba ta sauya ba: haɗa mutane a Intanet. Da Kuma samun maƙudan kuɗade daga talla.
Yayin da dandalin ke cika shekara 20, ga hanyoyi huɗu da Facebook ya canza duniya.
1. Facebook ya canza harkar sada zumunta
Sauran shafukan sada zumunta, irin su MySpace, sun fara aiki kafin Facebook - amma nan take shafin Mark Zuckerberg ya tashi bayan an ƙaddamar da shi a 2004, wanda ke tabbatar da yadda dandali irin wannan zai iya ɗaukan hankali cikin sauri.

ASALIN HOTON,MYSPACE
Tom shine abokin kowa na farko akan MySpace, wanda Tom Anderson ya ƙaddamar shekara guda kafin Facebook
A cikin ƙasa da shekara ɗaya masu amfani da shi sun kai miliyan daya, kuma a cikin shekara huɗu ya wuce MySpace - sakamakon fitar da sabbin abubuwa kamar 'tagging' mutane a hotuna.
Fita yawo da kyamarar zamani, sannan 'tagging' abokanka a cikin hotuna da yawa ya zama babban jigon rayuwar samari a ƙarshen shekarun 1990.
Ya zuwa shekarar 2012, masu amfani da shafin sun wuce biliyan daya kowanne wata, kuma, baya ga ɗan tuntuɓen da aka samu a ƙarshen shekarar 2021 - lokacin da masu amfani da shafin na yau-da-kullum suka ragu a karon farko zuwa biliyan 1.92, dandalin ya ci gaba da bunƙasa.
Ta hanyar faɗaɗa zuwa ƙasashen da ke da matsalar sadarwa da kuma ba da intanet kyauta, kamfanin ya ci gaba da riƙe tare da haɓaka yawan masu amfani da shafin Facebook. A ƙarshen 2023, Facebook ya ba da rahoton cewa masu amfani da shafin sun kai biliyan biyu a kullum.
Maganar gaskiya, Facebook ba shi da farin jini a tsakanin matasa kamar yadda ya ke a baya. Duk da haka, ya kasance mafi shaharar hanyar sadarwar zamantakewa a duniya, kuma ya haifar da sabon zamani na ayyukan zamantakewa a Intanet.
Wasu suna ganin Facebook da abokan hamayyarsa a matsayin abubuwan da ke ƙarfafa zamantakewa, wasu kuma suna ganin su a matsayin masu ruruta halayen lalata.
2. Facebook ya rage yadda mutane ke ɓoye sirrinsu
Facebook ya nuna yadda tattara bayanan abubuwan da muke so da waɗanda ba mu so ya zama abu mai matuƙar riba.

ASALIN HOTON,FACEBOOK
A kwanakin nan, kamfanin da ya mallaki Facebook, Meta, wani katafaren kamfanin talla ne wanda, tare da ire-irensu Google, ke ɗaukar kaso mafi tsoka na kudin talla a duniya.
Meta ya bayar da rahoton kusan dala biliyan 34 na kuɗaɗen shiga a cikin a tsakiyar 2023, musamman daga bai wa masu talla ayyukan talla da ke harin masu amfani da shafin kai-tsaye; An bayyana cewa an samu riba ta kudi dalar Amurka biliyan 11.5.
Sai dai kuma Facebook ya nuna inda tarin bayanai zai iya tabarbarewa.
An ci tarar Meta sau da yawa saboda kuskuren sarrafa bayanan sirri.
Al’amarin da ya fi fitowa fili shi ne badaƙalar Cambridge Analytica a shekarar 2014, wanda ya kai ga Facebook ya biya dala miliyan 725 don sasanta shari’a saboda wani gagarumin satar bayanai da ya gudana.
A cikin 2022, Facebook ya kuma biya tarayyar Turai tarar Yuro miliyan 265 saboda damar da ya bayar na fitar da bayanan sirri daga shafin.
Kuma a shekarar da ta gabata, Hukumar Kare Bayanai ta Ireland ta ci kamfanin tarar Yuro biliyan 1.2, saboda sauya wurin bayanan masu amfani da shafin a ƙasashen Turai zuwa wurin da ya zarce zarafinsu. A halin yanzu dai Facebook na ɗaukaka ƙara kan tarar.
3. Facebook ya shigo da harkar siyasa intanet
Ta hanyar bayar da tallace-tallace zuwa masu amfani kai-tsaye, Facebook ya zama babban dandalin yaƙin neman zaɓe a duniya.

ASALIN HOTON,REUTERS
Misali, a cikin watanni biyar gabanin zaɓen shugaban ƙasar Amurka na shekarar 2020, tawagar shugaba mai ci a lokacin Donald Trump ta kashe sama da dala miliyan 40 wajen tallace-tallace a Facebook, kamar yadda binciken Statista ya nuna.
Facebook ya kasance yana da hannu wajen sauya siyasar can ƙasa- ta hanyar bayar da dama ga ƙungiyoyin masu amfani da dandalin su taru, su gudanar da yakin neman zaɓe da kuma tsara ayyuka.
Rahotanni sun ce Facebook da Twitter sun taka muhimmiyar rawa a lokacin juyin-juya-halin ƙasashe Larabawa wajen taimakawa lokacin shirya zanga-zanga da yaɗa labaran abubuwan da ke faruwa a ƙasa.
An soki amfani da ake yi da Facebook domin gudanar da harkokin siyasa saboda irin abubuwan da kan iya biyo baya, ciki har da tasirin da ya ke da shi kan haƙƙin bil'adama. A cikin 2018, Facebook ya amince da rahoton Majalisar Dinkin Duniya wanda ya ce ya gaza hana mutanen da ke amfani da dandalin wajen "rura wutar tashe-tashen hankula" kan 'yan Rohingya a Myanmar.
4. Facebook ya ƙara wa Meta ƙarfi.
Da babbar nasarar da Facebook ya samu, Mark Zuckerberg ya gina dandalin sada zumunta da kuma daular fasaha wadda ba a taba ganin irin ta ba ta fuskar yawan masu amfani da kuma tasiri.

ASALIN HOTON,REUTERS
Kamfanoni masu tasowa, da suka haɗa da WhatsApp da Instagram da Oculus, duk an saye su ne a ƙarƙashin inuwar kamfanin Facebook, wanda ya canza suna zuwa Meta a cikin 2021.
Meta yanzu ya ce fiye da mutane biliyan uku suna amfani da aƙalla ɗaya daga cikin manhajojinsa a kowace rana.
Kuma lokacin da ya kasa siyan abokan hamayyarsa, ana zargin Meta da kwaikwayarsu - domin ya ci gaba da mamaye ko ina.
Siffar Labaru masu ɓacewa a Facebook da Instagram yayi kama da wani mahimmin fasalin da aka samu a Snapchat; Instagram Reels shi ne amsar kamfanin ga ƙalubalen da manhajar TikTok na raba bidiyo ya haifar; Kuma Threads shi ne ƙoƙarin Meta na kwaikwayon X, wanda aka fi sani da Twitter.
Dabarun sun zama mafi mahimmanci fiye da kowane lokaci, sakamakon ƙaruwar gasa da kuma ƙarin matsin lamba daga hukumomi masu sanya ido.
A cikin 2022, an tilasta wa Meta ya siyar da Giphy mai yin GIF duk da cewa zai yi hasara, saboda fargabar wuce gona da iri a sakamkon mamaye kasuwa.
Shekara 20 masu zuwa?
Ci gaban da Facebook ke samu na nuni da ƙoƙarin da Mark Zuckerberg ke yi na tabbatar da tasirin shafin.
Amma kiyaye kambinsa a matsayin mashahurin dandalin sada zumunta zai zama babban ƙalubale a cikin shekaru 20 masu zuwa.
Meta yanzu yana matuƙar yunƙuri don gina kasuwancinsa wurin haɗa ƙirƙirarriyar duniya ta Metaverse, wadda ake iya cewa ya sha gaban manyan abokan hamayyarsa kamar Apple.
Ƙirƙirarriyar basir ta AI shi ma abu ne da Meta ya mayar da hankali a kansa.
Don haka, yayin da kamfanin ya ci gaba da nisa daga tushen sa na Facebook, zai bayar da sha'awa a ga abin da zai faru a nan gaba da wannan shahararriyar manhajar.
(bbc hausa)
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Rikicin ECOWAS Na Iya Illata Nijeriya — Masana
Ficewar Nijar ya fi janyo damuwa musamman ga ’yan Nijeriya wadanda suke da al’adu da harshe da addini kusan daya.
Alamu na nuna cewa Nijeriya na iya tafka asara idan aka kwatanta da sauran kasashe 12 na Kungiyar Tattalin Arziki ta Kasashen Afirka ta Yamma (ECOWAS) ta fannin tsaro da tattalin arziki sakamakon ficewar kasashen Mali da Burkina Faso da Nijar daga kungiyar, kamar yadda wasu masana da wasu daga cikin al’ummomin da ke a kan iyakar kasar suka shaida wa Aminiya.
Sai dai wasu masana sun musanta cewa ficewar kasashen uku zai yi illa ga harkokin kasuwanci da tattalin arziki da zuba jari wanda hakan ka iya illata dokar kasuwanci ta Afirka (AfCFTA).
An samar da Dokar AfCFTA ce a matsayin wata hanya ta kasuwancin bai-daya a Afirka domin bunkasa ayyukan kasuwanci a nahiyar.
Idan ba a manta ba, sojojin da suka yi juyin mulki a kasashen uku, a ranar Lahadin makon jiya sun fitar da sanarwar ficewa daga Kungiyar ECOWAS.
Wannan ya biyo bayan takunkumin da kungiyar ta sa wa kasashen uku ne bayan hambarar da shugabannin dimokuradiya a kasashensu.
An dakatar da kasar Mali daga Kungiyar ECOWAS a shekarar 2021 bayan juyin mulki biyu da suka yi. Burkina Faso kuwa a shekarar 2022 ce aka dakatar da ita, sannan sai Nijar a shekarar 2023.
Duk da cewa dokar Kungiyar ECOWAS ta nuna dan kungiyar zai iya ficewa ce kawai bayan wa’adin shekara guda, amma wadanda suka tattauna da wakilanmu sun nuna al’amura ba sa daidaita masu ba tun a bara kuma suna ganin hukuncin da kasashen uku suka yanke zai kara ta’azzara lamarin ne maimakon saukaka musu.
Ba kamar abin da ya faro da Mali da Burkina Faso ba, dakatar da Nijar ya fi janyo damuwa musamman ga ’yan Nijeriya da kuma ’yan Nijar din wadanda suke da al’adu da harshe da addini kusan daya.
Babu wata rata mai yawa da ya raba kasashen a jihohin bakwai wanda hakan ya sa kasashen ke cudanya da juna cikin sauki.
Baya ga wasu ’yan takardun da ake cikewa, al’ummomin kasashen biyu ba sa bukatar biza wajen tsallakawa kasashen domin gudanar da kasuwancinsu ko mu’amalarsu ta yau da kullum.
Amma da aka sanya wa Nijar takunkumi a shekarar 2023 tare da sanya musu ido sun ji a jikinsu domin kowa hakan ya sa an rufe dukkan iyakokin kasashen biyu.
Matakain dai ya janyo karancin kayan abinci da bukatun yau da kullum a yankunan kan iyakan. Kasar ta Nijar ta dogara ce matuka daga kayan abinci da na gine-gine daga Nijeriya.
Ita kuwa Nijeriya tana dogara ce daga dabbobin da ake shigowa da su daga Nijar da suka hada da rakuma da tumaki da awaki da kuma dabino da sauransu.
Juyin mulkin soja da aka yi a Nijar da kuma matakan da Kungiyar ECOWAS ta dauka wanda Nijeriya ke shugabanta ya shafi hadin gwiwa wajen yaki da ta’adanci da kasashen biyu ke yi a kan iyakokinsu a Arewaci da Kudancin kasashen kamar yadda jami’an tsaron da ke aiki a kan iyakar Tafkin Chadi suka tabbatar.
A watan Nuwamba 2023 Aminiya ta ruwaito irin gibin da aka samu sakamakon wannan takaddama a tsakanin kasashen biyu wanda hakan ya janyo karuwar hare-haren a Tafkin Chadi.
Wasu wurare a kan iyakokin kasashen biyu musamman ta yankin Gaidam a Yobe da Malam Fatori da Damasak a Jihar Borno suna fuskantar karuwar hare-haren ’yan ta’adda.
A cewar majiyoyinmu a Gaidam, kasar Nijar ta janye sojojinta daga iyakar kasar ta Gaidam wanda ya janyo karuwar hare-haren.
’Yan gudun hijirarmu na cikin kaka-ni-ka-yi — Gwamnatin Borno
Shugaban Kungiyar Dattawan Jihar Borno Dokta Bulama Mali Gubio ya ce idan aka yi la’akari da kawancen da ke tsakanin kasashen biyu, janyewar Nijar daga ECOWAS zai yi illa ga harkokin kasuwanci a Nijeriya da kuma ’yan gudun hijirar Nijeriya da ke Nijar.
“Muna magana ce a kan kasuwancin da ke gudanar a kan iyakokin kasashen biyu ba ’yan fasa kwauri ba.
“Yanzu mutanenmu dole sai sun nemi biza kafin tsallakawa cikin Nijar. Yanzu babu maganar shiga yadda aka ga dama da kayayyakin abinci,” in ji shi.
Ya yi kira ga ’yan Nijeriya da ke a kan iyakokin Nijar da su goyi bayan matakin da Shugaban Kasa Bola Ahmed Tinubu zai dauka da kuma kungiyar ta ECOWAS wajen yin amfani da tattaunawa domin magance matsalar.
“Ko babu komai ’yan Arewa su yi abin da za su iya yi domin tabbatar da an kare kasancewarsu da aka kulla shekaru masu yawan gaske.
“Sarakunanmu da malamanmu da da tsofaffin shugabannin kasashen da kuma ’yan kasuwarmu duk sun yi kokarinsu wajen tabbatar da an samu zaman lafiya, amma sojojin sun ki ta hanyar ci gaba da rike mulki duk kuwa da talakawan ba sa so,” in ji shi.
Haka kuma wata majiyarmu a cikin jami’an tsaro a kan iyakar Abadam wanda gari ne da ke kan iyakar kasashen biyu inda dubban ’yan Nijeriya ke gudun hijira a Diffa, Nijar ta ce an fara samun masu komawa gida da yawa.
“’Yan gudun hijira ’yan Nijeriya da ke dawowa daga Diffa da wasu yankuna na Nijar akwai damuwa.
“Yawancin lokuta muna tura su ne zuwa sansanin ’yan gudun hijira da ke Monguno.
“Yanzu haka sansanin a cike yake makil wasu ba su da wurin kwanciya sannan babu isasshen abinci ga wadanda ke sansanin,” in ji majiyar.
Abdullahi Ibrahim wanda lauya ne kuma mai kare haƙƙin mutane a Maiduguri ya ce a yayin da Nijar ta dogara da Nijeriya a fannin tattalin arziki ita ma Nijeriya ta dogara da Nijar ta fannin yaki da ’yan ta’adda musamman Boko Haram.
“Mutane a Malam Fatori suna shiga Maine Soroa a Nijar domin neman magani. Suna kuma sayen kayan bukatun yau da kullum kamar ruwan sha da kayan abinci saboda ya fi sauki da su zo Maiduguri ko Mongono,” in ji shi.
Wani jami’in tsaro da ke aiki a Arewa maso Gabas wanda ba ya so a ambaci sunansa ya ce, “Muna bukatar goyon bayan Nijar domin kawar da ’yan ta’adda musamman a Abdam da Kukawa da Marte da Tunbus a yankin Tafkin Chadi,” in ji shi.
Ya ce, “ISWAP ana ganinsu a yankin Gashegar da Arkubma da Shilay inda suke tsayawa domin kai hare-harensu da kuma karbar haraji a wajen al’ummomin yankin.
“Ko a kwanakin nan ISWAP sun fito da motoci biyu da babura shida inda suka kwana a kauyen Late da safe suka dan yi zagaye a cikin garin a kusa da Kareto da Laye.
“Yawancin ’yan kungiyar ISWAP sun fito ne daga yankin Gaidam. Wannan yankin na karkashin Karamar Hukumar Mobbar ce,” in ji shi.
Matakin zai kara jefa mu cikin wahala — Mazauna Yankunan Katsina
Da suke bayani a kan lamarin da ke faruwa a kan iyakokin kasashen biyu, Shugaban Kungiyar Al’ummar Jibiya, Alhaji Hide Dahiru ya ce al’amuran kasuwanci suna cikin wani yanayi a yankin, inda ya ce ficewar kasahen uku za ta kara ta’azara lamarin a yankin.
“Akwai dokokin kan iyakokin kasashen da cike da shigi da fice domin gudanar da kasuwanci.
“Yanzu da wadannan kasashen suka fice daga ECOWAS hakan ya nuna ke nan wadannan dokoki ba za su yi amfani ba sababbi za a fito da su.
“Kamar yadda ka sani akwai kayayyaki irin su hatsi da dabino da ake samu daga Nijar da ba a biya musu haraji.
“Idan wannan mataki ya jima ya zama ke nan wadannan kayayyaki za a sanya su cikin wadanda ake safararsu ke nan,” in ji shi.
Wani masanin tsaro Muhammad Nasir Abdullahi ya ce akwai hadin gwiwa a tsakanin Nijar da Nijeriya wajen yaki da ta’adanci a kan iyakokin kasashen biyu, inda ya ce idan aka tsinke shi lamarin zai lalace.
Dangane da zamantakewa kuwa ya ce akwai mu’amala sosai a tsakanin mazauna iyakar kasashen biyu daga auratayya wanda kuma tsaurara matakan zai iya shafar wannan mu’amala ta iyalai.
Hadin kan kasashen na cikin barazana — Farfesa
A cewar Farfesa Tanko Baba masanin siyasa a Jam’iar Usman Dan Fodiyo da ke Sakkwato, matakin zai fi illa wa Nijeriya.
“Nijeriya ce a kan gaba wajen batun ECOWAS. Nijeriya ce ta fi yawan jama’a a cikin kasashen 15.
Kasuwancin Arewacin Nijeriya har cikin Nijar da Mali da Burkina Faso, ke nan kasuwancin da ke tsakanin wadannan kasashe uku zai lalace.
“Ina son ka sani cewa tattalin arzikin Nijeriya a fannin kasuwancin dabbobi kusan kaso 69 zuwa 79 na dabbobin da ke shigowa Nijeriya daga Nijar ne.
“Wasu ma ba daga Nijar kadai suke ba wasu daga Senegal ne a kullum. A yanzu ke nan za a samu nakasu a fannin.
“Bayan matsalar tsaro da muke fama da ita a yankin Arewa. A tarihi Nijeriya ba ta da makwabciya da ke biyayya gare ta kamar Nijar.
“Yanzu ke nan Nijeriya na iya fuskantar barazanar matsalar tsaro a yankin.
“Yanzu Nijar ta fice kuma ’yan ta’addar nan da barayin shanu duk suna da asali da irin wadannan kasashe irin su Mali da Burkina Faso da Nijar,” in ji shi.
Dokta Bashir wanda shi ma masanin tattalin arziki ne a Jami’ar Usman Dan Fodiyo ya ce kasuwanci a tsakanin Nijar da Mali na da girma.
“Idan ka je kan iyakar kasashen nan ka ga irin kasuwancin da ke faruwa a can za ka fahimci cewa mutane da yawa sun dogara da wadannan kasashe wajen kasuwancinsu, ficewar kasashe uku ba karamar matsala ba ce,” in ji shi.
Ya ce kuɗaɗen da ke shigowa a dalilin kasuwanci a tsakanin Nijar da Nijeriya ya kai Dalar Amurka biliyan daya a bara.
(AMINIYA)
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
An Sako Daliban Da Aka Yi Garkuwa Da Su Ekiti
An sako daliban da malaman nasu ne kimanin mako guda bayan an yi garkuwa da su
Dalibai tara da malamansu da aka yi garkuwa da su a Jihar Ekiti sun kubuta daga hannun ’yan bindiga.
Da misalin karfe 2 na dare, kafin wayewar garin yau Lahadi ne masu garkuwa da su suka sako su.
Hukumomi a jihar sun tabbatar da sako daliban su tara tare da malamansu.
An sako daliban da malaman nasu ne kimanin mako guda bayan an yi garkuwa da su a makarantar Apostolic Faith Group of Schools da ke yankin Emure-Ekiti.
Kawo yanzu dai babu bayanin ko an biya kudin fansa.
An yi garkuwa da su ne a makarantar Apostolic Faith Group of Schools da ke yankin Emure-Ekiti.
(AMINIYA)
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Saturday, 3 February 2024
INEC Ta Dakatar Da Sake Zabe A Enugu, Kano, Akwa Ibom Sakamakon Rikici, Sace Jami'an Zabe
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Labari Da Dumiduminsa: NAHCON Ta Sanar Da Kudin Hajjin 2024
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Wednesday, 24 January 2024
Har Yanzu 29 Ga Watan Afurilu Ce Ranar Karshe Ta Rufe Yin Bizar Hajin 2024 - Laminu Rabi'u Danbaffa
Welcome to Alheekmah News Alheekmah News is a Nigerian digital news platform committed to delivering timely, accurate, and credible news to readers across Nigeria and beyond. We provide comprehensive coverage of national affairs, politics, governance, Hajj and Umrah, religion, education, business, security, health, and other issues that shape our society. Our mission is to inform, educate, and inspire through responsible journalism founded on accuracy, fairness, and integrity. We strive to provide factual reporting while promoting public awareness and constructive engagement. At Alheekmah News, we believe that reliable information empowers individuals and strengthens communities. We are dedicated to bringing you breaking news, in-depth reports, exclusive interviews, and insightful analysis you can trust. Stay informed. Stay connected. Stay ahead with Alheekmah News.
Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa
FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy
The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...
-
Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emefiele, ya ce Bankuna za su ci gaba da karbar tsoffin takardun kudi na Naira ko da baya...
-
Matar hamshakin dan kasuwa na Kano, Alhaji Aminu Alasan Dantata, Hajiya Rabi ta rasu Jaridar SOLACEBASE ta rawaito cewa, Hajiya ...
-
Zababben Gwamnan Jihar Kano Ya Sanar Da Kwamitin Karbar Mulki …… Dr. Baffa Bichi, Abdullahi Musa ya nada a matsayin Shugaba da Sakatare Baya...


