Search This Blog

Sunday, 19 March 2023

Hukumar Zabe Ta Sanar Da Abba K Yusuf A Matsayin Wanda Ya Lashe Zaben Gwamnan Kano

Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa INEC ta bayyana Abba Kabir Yusuf na jam'iyar NNPP  a matsayin wanda ya lashe zaben gwamnan Kano da aka kammala kwanan nan da kuri'u 1,019,602.

Thursday, 16 March 2023

Za Mu Kama Duk Wanda Ya Dauki Makami Ranar Zabe A Kano —’Yan Sanda

 


Mataimakin babban sufeto-Janar na ’yan sanda DIG Hafiz Muhammad Inuwa da ke kula da harkokin zaben shekarar 2023 a yankin jahohin Arewa maso Yammacin Najeriya, ya gargadi ’yan siyasa da magoya bayansu, da su kauce wa yin wani abu da zai tada hankulan masu zabe. 

DIG Hafiz M. Inuwa ya bayyana cewa shugaban ’yan sanda Usman Alkali Baba ya umarce su, da su gargadi ’yan siyasa da masu ruwa da tsaki da su ja wa magoya bayansu kunne gabanin zaben da ke tafe a ranar Asabar 18 ga watan Maris 2023.

Ya bayyana hakan ne a Jihar Kano, a ci gaba da shirye-shirye da rundunar ke yi na tabbatar da tsaro da kare rayukan al’umma da kuma dukiyoyinsu.

Ya kara da cewa fatansu, shi ne a yi zabe lafiya a kammala lafiya, ba tare da nuna siyasa da gaba ba.“Duk wani dan siyasa in dai yana son ci gaban Kano, to zaman lafiya shi ne ci gaban, so ake a zauna lafiya.

“Kuma na zo da jawabi, in gargade su, Wallahi ba za mu yi kasa a gwiwa ba wajen maganin duk wani da ya nemi ya tada fitina,

“Saboda haka ina tabbatar muku da cewa duk wanda ya nemi ya dau makami ko don ya hana wani fitowa zabe, ko don ya jikkata wani, to Wallahi Tallahi fushin hukuma ne a tattare da shi” in ji shi.Ya ce ba zu raga wa kowa ba duk girmansa kowaye , domin ci gaban Nijeriya da ci gaban Kano da kuma zaman lafiya shi ne agaban mu.

Tun kafin wannan lokacin ne Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa ya bayyana cewa sun tanadi ’yan sanda masu yawa don tabbatar da tsaro a zaben ranar 18 ga watan Maris 2023.

Sai Buhari Ya Yi Magana Za Mu Karbi Tsohon Kudi —’Yan Kasuwa


 ’Yan kasuwa a wasu yankunan Najeriya sun bayyana cewa ba za su fara karbar tsoffin takardun N5oo da N1,000 har sai sun ji Shugaban Kasa Muhamamdu da bakinsa ya ce su fara karba.

’Yan kasuwa da kwastomominsu jihohin Kaduna da Legas da kananan hukumomin Abaji da Kwali a Yakin Babban Birnin Tarayya na kin karbar tsoffin kudin ne, a washgarin da bankunan kasuwanci suka fara bayar da su, bisa umarnin Babban Bankin Najeriya (CBN).

Sai dai a Jihar Kano, harkokin kasuwanci sun fara komawa yadda aka saba, tun bayan da bankuna suka fara bayar da tsoffin kudi, kuma mutane suka ci gaba da amfani da su a harkokin kasuwanci.

Harkoki sun fara kankama a Kano

Wani tan kasuwa a Kasuwar Kantin Kwari da ke Kano, Adamu Hamza, ya ce sun fara samun karuwar ciniki,  “tsakanin jiya (Talata) da yau (Laraba), kudi ya fara yawo a hannun jama’a, suna kawowa kuma muna karba.”

Aminiya ta ruwaito cewa tun ranar Talata injinan ATM a birnin Kano suka fara bayar da tsoffin kudin, sai dai yawanci N500 ne.

Haka kuma an samu raguwa mutane da ke neman cirar kudi, dai dai wasu bankunan sun bayyana cewa tsabar kudin da ke hannunsu  ya kare, shi ya sa ba a ganin layin mutane a ATM dinsu domin cirar kudi.

‘Sai mun ji daga bakin Buhari’

Aminiya ta zaiyarci yankin Abaji a ranar Laraba, inda ta iske mutane na ta gunaguni cewa bankuna sun koma ba wa mutane tsoffin takardun kudin.

Wani dan kasuwa, Bashir Aliyu, ya yi mana korafin cewa ya ce cikin banki cirar kudi , amma aka ba shi tsoffin takardun N1,000 da aka sauya, amma ya ki karba, sabo ba zai iya kashe su cikin sauki ba, idan ya je kasuwannin kauye.

A cewarsa, duk da cewa CBN ya ba umarnin bankuna su ci gaba da harkokinsu da tsoffin kudin, shi ba zai samu natsuwa ba sai sai ya ji Shugaba Buhari da kansa ya yi wa ’yan kasa magana cewa su ci gaba da amfani da tsoffin kudin.

Wani jami’in banki da ya nemi mu boye sunansa ya shaida mana cewa bankin ya fito da Naira dubu 500 na tsoffin takardun kudi da yake da su domin ba wa mutanen da suka zo cirar kudi, amma yawancin mutanen sun ki karba.

“A takaice, daga cikin N500,000 da bankin ya fitar domin ba wa kwastomomi N150,000 kadai aka samu wadanda karba,” in ji jami’in bankin.

Hakazalika wasu ’yan kasuwa a yankin Kwali na kin karbar tsoffin kudin, saboda har yanzu ba su ji Shugaba Buhari ya yi magana a kai ba.

Wata ’yar kasuwa mai suna Misis Laraba Gwatana ta ce, “Ni ba zan karbi tsohon kudi ba, saboda har yanzu rade-radi muke ji cewa CBN ya umarci bankuna su koma bayar da tsoffin kudaden.

“Amma ni dai ba zan karbe su ba, sai lokacin da na ji Buhari ya fito ya yi wa ’yan Najeriya jawabi cewa su rika karbar tsoffin kudin; gaskiya ba wanda ke so ya kara yin asara.”

’Yan kasuwa kaduna ma haka

Zuwa ranar Laraba, ’yan kasuwa da dama a Jihar Kaduna na kin karbar tsoffin takardun N500 da N1,000 a Kasuwar Sheikh Gumi, inda suke bayyana fargaba kan batun amfani da tsoffin kudaden.

Wakilinmu ya lura cewa maimakon karbar tsoffin kudaden, ’yan kasuwa da dama sun tanadi na’uarar tura kudi ta PoS ga kwastomominsu.

Wani dan kasuwa mai sayar da kayan gwari, Malam Lawal Ibrahim, ya shaida wa Aminiya cewa, “ban fara karbar tsoffin takardun N500 da N1,000 tukuna; amma ina karbar tsohuwar N200.”

Ya ce dalilinsa shi ne, “Gwamnati na ta kumbiya-kumbiya, don haka ina tsoron in karba, daga baya CBN ya ce ya canza shawara a bar ne da asarar biyan kudin kaya, shi ya sa ba na karba.”

Mohammed Isa mai kayan gwari shi ma ya ce, gara ya ki karbar tsoffin kudaden da ya bari su ja masa asara.

“Lokacin da aka fara cewa mu kai tsoffin kudin CBN, sai da na yi kwanaki a kofar CBN don in ajiye N100,000. Shi ya sa na yi wa kaina riga-kafi, da in yi asara gara kaya na sun yi kwantai.”

Yankin Kudu

Wannan yanayi haka yake a wasu sassa na Jihar Legas, inda bakuna suka fara bayar da tsoffin kudin, amma na dar-dar wajen yin cinikayya da su, duk kuwa da umarnin CBN na ci gaba da amfani da su zuwa ranar 31 ga watan Disamba.

A Jihar Ribas kumma, manyan shaguna da gidajen mai da wasu wuraren kasuwanci na ci gaba da harkokinsu da tsoffin kudin.

Sai dai an korafi cewa duk da cewa bankuna na bayar da tsofifn kudaden, amma idan aka kai musu ba sa amsa.

Wata mazauniyar garin Fatakwal, Amaka Ike, wadda wakilinmu ya zanta da shi ya ce, ta ce da kyar ta iya yin sayayya da tsofifn kudaden.

Amaka ta ce, “wasu masu shaguna, gidajen mai da wasu ’yan kasuwa ba sa karbar tsoffin kudaden saboda a cewarsu, har yanzu ba su natsu ba, gwamnati za ta iya sauya shawara a kowane lokaci, kan batun.”

AMINIYA

DSS ta kama mutum biyu a Kano kan zargin tayar da rikici

 


Hukumar tsaro ta farin kaya DSS ta ce ta kama wasu mutane biyu da take zargi da tunzura mutane domin tayar da hankali a jihar Kano gabanin zaɓen gwamna da na ‘yan majalisun jiha da za a yi a ranar Asabar.

 

Cikin wata sanarwa da ta wallafa a shafinta na Twitter hukumar ta DSS ta ce mutanen sun naɗi hoton bidiyo ne da suke bayanan tunzura jama’a a cikinsu, sannan suka riƙa wallafa shi a shafukan sada zumunta.

 

Ta kuma wallafa sunayen Sharu Abubakar Taɓule mai shekara 37 a duniya, da kuma Isma’il Iliyasu Mnagu mai shekara 51 a matsayin waɗanda ta kama.

 

“Cikin waɗannan saƙonnin masu haɗari, sun nuna jam’iyyar siyasar da suke goyon baya kuma suka yi kira ga magoya bayansu su kai wa abokan hamayyarsu hari duk inda suka gansu.

 “Waɗanda ake zargin sun yi kira da a kai wa jami’an tsaro hari yayin zaɓen gwamnoni da na ‘yan majalisar jihohi da za a yi a ranar Asabar.


“Wata jam’iyyar siyasa a Kano na barazanar shirya zanga-zanga a sakamakon shirin kai hare-haren,” in ji hukumar ta DSS.


Sanarwar ta ƙara da cewa jam’iyyar siyasar ta shirya kutsawa ofisoshin wasu hukumomin tsaro a ranar 16 ga watan Maris a matsayin nuna goyon baya ga waɗanda ake zargin.“Yayin da hukumar ke sanar da mutane kan wannan haramtaccen mataki, ta kuma yi kira ga jam’iyyar da ta dakatar da wannan lamari, ko kuma ta shirya yaba wa aya zaƙinta.


“DSS ba za ta zuba ido tana kallon mutane suna tunzura al’umma ba su tayar da hankali da rashin tsaro a jiha ba.”


Sanarwar DSS ta ce za ta haɗa hannu da sauran hukumomin tsaro domin tabbatar da an samar da cikakken tsaron da zai bayar da damar da gudanar da zaɓe mai inganci a jihar.


Baya ga Kano hukumar tsaron ta kama wasu mutane da ke irin wannan kiraye-kiraye a wasu jihohi a faɗin ƙasar.


Hukumar ta shawarci jam’iyyun siyasa a fadin Najeriya da su gargadi mabiyansu su zama masu bin doka da oda, domin tabbatar da dimokuraɗiyya ta samu wurin zama yadda ya kamata


BBC

Tuesday, 14 March 2023

‘Kusan Sau Miliyan 13 Aka Yi Yunkurin Yi Wa Najeriya Kutse Yayin Zaben Shugaban Kasa’


 Gwamnatin Tarayya ta ce akalla sau 12,988,978 aka yi yunkurin yin kutse a shafukan intanet na Najeriya yayin zaben Shugaban Kasa da na ’yan Majalisun Tarayya da aka yi a ranar 25 ga watan da ya gabata.

Hare-haren, a cewar gwamnatin an kai su ne daga ciki da wajen kasar, kuma an yi su ne kan shafukan gwamnati, kusan sau 1,550,000 a kullum.

Ministan Sadarwa, Isah Ali Pantami ne ya sanar da hakan a cikin wata sanarwa ranar Talata.

To sai dai ya ce yunkurin kutsen ya yi tashin gwauron zabo zuwa sau 6,997,277, a ranar zaben Shugaban Kasa ta Asabar.

Ministan ya kuma ce ma’aikatarsa ta kafa wani kwamitin yaki da irin wadannan hare-haren, kuma ya fara aiki ne ranar 24 ga watan na Fabrairu, sannan ya kammala ranar 28.

AMINIYA

Sufeto Janar Ya Sake Turo Usaini Gumel A Matsayin Sabon Kwamishinan 'Yan Sanda Na Kano


Sufeto Janar na ‘yan sanda, Usman Alkali, ya sake soke turo kwamishinan ‘yan sandan Kano.

A wata sanarwa da aka fitar a ranar Litinin, Sufeto Janar din ya soke aika Feleye Olaleye a matsayin kwamishinan ‘yan sandan Kano tare da sanya CP Ahmed Kontagora a matsayin wanda zai maye gurbinsa.

Sai dai a wata siginar da aka sake fitarwa a daren jiya, sufeto janar din ya nada CP Usaini Gumel a matsayin wanda zai jagoranci rundunar 'yan sanda ta Kano lokacin zabukan gwamnoni da na ‘yan majalisar jiha a jihar.

A ranar 8 ga Maris, bayan zanga-zangar da ‘yan adawa suka yi, IGP ya sauya matakin da aka tura CP Balarabe Sule, tsohon babban jami’in tsaro ga gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje, a matsayin wanda zai maye gurbin CP Mohammed Yakubu

A cikin sabuwar takardar da aka fitar mai dauke lamba TH.5361/FS/FHQ/AB3/SUB.6/146, Mista Alkali kuma ya sake yin wasu ƙananan canje-canje a cikin umarnin.

IGP ya umurci DCP Auwal Musa da ya karbi DCP Nuhu Darma a matsayin mataimakan kwamishinan ‘yan sanda mai kula da ayyuka da binciken manyan laifuka (CID)

Daily Nigerian 

Dokar Zabe Ta Inganta Zabukan Najeriya —Fadar Shugaban Kasa

 


Fadar Shugaban Kasa ta ce zabukan da aka yi na Shugaban Kasa da ’yan Majalisar Dokokin Tarayya a ranar 25 ga watan Fabarairu, sun inganta ne albarkacin Dokar Zabe ta 2022.

Mai magana da yawun Shugaban Kasa, Malam Garba Shehu, ya ce albarkacin Dokar Zabe, an samu gagarumin ci gaba idan aka kwatanta da zabukan da aka yi a kasar a baya.

A sanarwa da kakakin shugaba Buhari ya fitar, fadar ta ce duk da cewa an samu wasu matsaloli nan da can, wannan ba zai sa a ce zaben ya gaza ba.

Fadar shugaban ta nuna godiya kan damuwar da manyan jagororin masu sanya ido na kasashen waje musamman tsoffin jakadu; Mark Green da Johnnie Carson suka nuna a kanmatsalolin da aka samu kan kayan aiki a lokacin zabukan.Sanarwar ta ce duk da ’yan matsalolin da aka samu ba za a ce zaben ya gaza ba, illa dai wadanda suka fadi ne suke nuna gazawarsa.

Kakakin ya ce zaben na Najeriya ba shi kadai ba ne ake samun ire-iren wadannan matsaloli abu ne da kusan a kowa ce kasa ake iya samu a zabe.

Malam Garba ya ci gaba da cewa “ko ba komai, yadda Ma’aikatar Harkokin Waje ta Amurka da Firaministan Birtaniya, Rishi Sunak da sauran shugabannin Afirka ta Yamma da na Tarayyar Afirka suka taya murna ga dan takarar APC Bola Ahmed Tinubu, wanda ya yi nasara a wannan zabe da ya kasance wanda aka fi fafatawa a tarihin Najeriya, hakan ya nuna cewa abin a yaba ne“Tabbas Dokar Zabe ta 2022 ta inganta zaben, la’akari da yadda na’urar tantance masu zabe BVAS ta kawo karshen aringizon kuri’u da duk wata cuwa-cuwa wajen kada kuri’a.”

AMINIYA

Monday, 13 March 2023

Labari da dumiduminsa : Bankin CBN Ya Ce Za A Ci Gaba Da Amafani Da Tsofaffin Kudi Na Har Zuwa 31 Ga Disamba


Babban Bankin Najeriya (CBN) ya ce tsofaffin takardun kudi na N200, N500 da N1000 suna nan a kan doka har zuwa ranar 31 ga Disamba, 2023.

Kakakin CBN, Isa Abdulmumin ne ya sanar da hakan a wata sanarwa da ya fitar a yammacin ranar Litinin.

“A bisa bin ka’idar da aka kafa ta bin umarnin kotu da kuma biyan ka’idar bin doka da oda da gwamnatin shugaban kasa Muhammadu Buhari ta yi, da kuma karawa ayyukan Babban Bankin Najeriya (CBN), a matsayin mai kula da Deposit. An umurci bankunan kudi da ke aiki a Najeriya da su bi hukuncin da kotun koli ta yanke na ranar 3 ga Maris, 2023,” in ji sanarwar.


“A bisa haka, CBN ya gana da kwamitin ma’aikatan banki inda ya ba da umarnin cewa tsofaffin takardun banki na N200, N500 da N1000 su ci gaba da zama a kan takardar kudi tare da sake fasalin kudin har zuwa ranar 31 ga Disamba, 2023.

Shugaba Buhari Yace, Bai Umarci Atoni Janar Da Gwamnan CBN Kan Kin Bin Umarnin Kotu Ba Dangane Batun Tsofaffin Kudi

 
Fadar shugaban kasa na son mayar da martani kan wasu damuwar da jama’a ke ciki na cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari bai mayar da martani ga hukuncin da kotun koli ta yanke kan batun kudin tsohon naira 500 da naira 1,000 ba, kuma ta bayyana a nan karara da cewa babu wani lokaci da ya umurci Babban Lauyan gwamnati da Gwamnan CBN su bijirewa duk wani umarnin kotu da ya shafi gwamnati da sauran bangarorin.

A sanarwar da babban mataimaki na musamman ga shugaban kasa kan harkokin yada labarai, Malam Garba Shehu ya fitar, ta ce, tunda aka rantsar da shugaban kasa a shekarar 2015, bai taba umurtar kowa da ya bijirewa umarnin kotu ba, bisa akidar cewa ba za mu iya gudanar da mulkin dimokuradiyya ba tare da bin doka da oda ba, kuma jajircewar gwamnatinsa kan wannan ka’ida ba ta canja ba.

Bayan zazzafar muhawarar da ake ta yi game da bin doka da oda dangane da halaccin tsohon takardun kudin, don haka fadar shugaban kasar na son bayyana karara cewa Shugaba Buhari bai yi wani abu da gangan ba na tsoma baki ko kawo cikas ga gudanar da shari'a.

Shugaban kasa ba karamin Shugaba ba ne, don haka ba zai hana babban lauyan gwamnati da gwamnan babban bankin kasar CBN yin cikakken bayanin ayyukansu kamar yadda doka ta tanada ba. A kowane hali. ana tafka muhawara a wannan lokaci idan aka samu hujjar kin amincewa da gangan da su biyun suka yi bisa umarnin kotun koli.

Umarnin shugaban kasa, bayan taron majalisar jiha. shi ne dole ne Bankin ya samar da duk kudaden da ake buƙata don rarrabawa kuma babu abin da ya faru da ya canza matsayi.

Tabbatacciyar hujja ce cewa
 Shugaban kasa cikakken mai mutunta tsarin shari'a ne da ikon kotuna. Babu wani abu da ya yi a cikin shekaru takwas ko fiye da suka gabata don yin ta kowace hanya don kawo cikas ga gudanar da shari'a, haifar da rashin amincewa da gudanar da shari'a, ko yin katsalandan ko lalata kotuna kuma babu wani dalilin da zai sa ya yi. don haka yanzu lokacin yana shirin barin ofis.

Mummunan yakin neman zabe da hare-haren da ‘yan adawa ke kaiwa shugaban kasa da duk wani nau’in masu sharhi ba daidai ba ne da kuma rashin adalci, domin babu wani umarnin kotu a kowane mataki da aka ba shi ko kuma aka ba shi umarni.

Dangane da tsarin rashin kudi da CBN ya kuduri aniyar samar da shi, sanannen abu ne cewa da yawa daga cikin ‘yan kasar da ke fama da wahalhalun da ake fama da su, abin mamaki suna goyon bayan manufar ganin cewa matakin zai dakile cin hanci da rashawa, da yaki da ta’addanci. gina yanayi na gaskiya da kuma karfafa jagoranci marar lalacewa na shugaban kasa.

Don haka ya dace a dora wa Shugaban kasa alhakin cece-kucen da ake fama da shi a halin yanzu kan karancin kudi, duk kuwa da hukuncin da Kotun Koli ta yanke. CBN ba ta da dalilin kin bin umarnin kotu bisa uzurin jiran umarni daga shugaban kasa.

Shugaba Buhari ya kuma yi watsi da ra'ayin cewa ba shi da tausayi, yana mai cewa "babu wata gwamnati a tarihinmu na baya-bayan nan da ta bullo da tsare-tsare don taimakawa masu rajin tattalin arziki da marasa galihu kamar wannan gwamnati mai ci."
 

Saturday, 11 March 2023

Dan Jarida Ya Mutu Yana Tattakin Zuwa Wurin Aiki Saboda Karancin Takardun Kudi

 


Wani fitaccen dan jarida da ke aiki a gidan rediyon Ibadan, ya riga mu gidan gaskiya a kan hanyarsa ta zuwa wurin aiki a safiyar wannan Asabar din.

Ma’aikacin jaridar wanda aka fi sani da Baba Bintin, ya yanke jiki ne ya fadi matacce kamar yadda wakilinmu ya ruwaito.

Bayanai sun ce lamarin ya faru ne yayin da Baba Bintin ke hanyarsa ta zuwa gidan rediyon Fresh FM, inda zai gabatar da wani shiri tare da wasu takwarorinsa, Komolafe Olaiya da Olalomi Amole a yankin Challenge da ke Ibadan, babban birnin Jihar Oyo.

Baba Bintin dai ya shahara wajen gabatar da shirin bayyana farashin kayayyaki da ranakun cin kasuwannin yau da kullum a fadin jihar da kewaye.

Jama’a a Najeriya na ci gaba da babatu kan halin kunci da suka shiga tun bayan sauya fasalin takardun kudi da Babban Bankin Kasar CBN ya yi.

CBN dai ya sauya fasalin takardun kudi na N200, da N500 da kuma N1,000 tare da dakatar da amfani da tsofaffin takardun kudin, lamarin da wasu gwamnoni suka kalubalanta a Kotun Koli 

A kan hakan ne Kotun Kolin a farkon wannan wata na Maris ta ba da umarnin ci gaba da amfani da tsoffin takardun kudin har zuwa ranar 31 ga watan Disamba, 2023.

Sai dai har yanzu Gwamnatin Tarayya ta shafa wa idonta kwalli a kan hukuncin, amma dai an samu wasu bankuna da suka soma bai wa abokanan huldarsu tsofaffin takardun kudin kamar yadda Kotun Kolin ta yanke.

AMINIYA

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...