Search This Blog

Friday, 6 January 2023

Al Nassr za ta mutunta hukuncin dakatarwar wasanni 2 kan Ronaldo

 


Kungiyar kwallon kafa ta Al Nassr a Saudi Arabia ta tabbatar da shirin mutunta hukuncin hukumar kwallon kafar Ingila kan sabon dan wasan da kungiyar ta saya Cristiano Ronaldo game da haramcin wasanni biyu da ke kansa

Wani jigo a Al Nassr ya shaidawa AFP yau juma’a cewa tauraron na Portugal mai shekaru 38 ba zai taka leda a wasanni biyu da kungiyar za ta doka nan gaba ba, domin mutunta hukuncin.  

Tun a watan Nuwamba ne dai, hukumar FA ta dakatar da Ronaldo a wasanni biyu saboda samunsa da laifin jifan wani magoyin bayan Everton da wayar salula lokacin da ya ke shirin daukar hotonsa bayan rashin nasarar Manchester United hannun Everton a Goodison Park.

Har zuwa yanzu dai Al Nassr ba ta yiwa Ronaldo rijista ba, kasancewar kungiyar ta zarta adadin ‘yan wasa 8 sa hukumar kwallon kafar Saudiya ta sahale mata saye daga ketare duk kaka.

Zuwa yanzu dai Al Nassr ta sayi ‘yan wasan da yawansu ya kai 9 daga ketare ciki har da Ronaldo da ta sayo kan yuro miliyan 200 bayan dan wasan gaban na Portugal ya raga gari da Manchester United ana tsaka da gasar cin kofin Duniya

Kwantiragin dan wasan mai shekaru 38 zai kaishi har zuwa watan Yunin 2025.

Yanzu haka dai Al Nassr na bukatar raba gari da dan wasa guda gabanin baiwa Ronaldo damar samun gurbi a Club din yayinda ake jita-jitar yiwuwar kungiyar za ta rabu ne da Jaloliddin Masharipov don samun gurbin yiwa tauraron na Portugal da ya lashe Ballon d’Or sau 5 rijista.

Bamu kai Karar Shugaban INEC Kotu ba - DSS

Hukumar Tsaro ta Farin Kaya (DSS) ta musanta labarin da ke yawo cewa tana cikin hukumomin tsaron da suka maka Shugaban Hukumar Zabe ta Kasa (INEC) Farfesa Mahmood Yakubu a kotu.

Kakakin rundunar, Peter Afunanya ne ya bayyana hakan a ganawarsa da manema labarai, inda ya yi karin haske kan umarnin wata Babbar Kotun Abuja na hana hukumomin tsaro ciki har da DSS din kama Yakubu.

Boka ya mutu yana lalata da matar fasto
Mun gano wadannin macizai a dajin Ecuador —Masana
A ranar Laraba ce dai Alkalin Kotun, M. A. Hassan ya ki amincewa da bukatar tsige shugaban INEC din daga mukaminsa, saboda zargin kin bayyana ainihin kadarorin da ya mallaka.

Alkalin ya ce kadarorin da Yakubun ya bayyana haka suke, kuma sun yi daidai da tanadin dokokin Najeriya.

Hukuncin dai ya biyo bayan karar da Somadina Uzoabaka ta shigar da Babban Lauyan Gwamnatin da Farfesa Yakubu mai lamba FCT/HC/GAR/CV/47/2022 don tilasta wa shugaban hukumar ta INEC sauka daga matsayinsa, har sai an gudanar da binciken wasu zarge-zargen da hukumomin tsaro daban-daban ke yi masa.
Sai dai Afunanya ya ce kwata-kwata DSS ba ta cikin hukumomin tsaron da suka shigar da waccan karar.

“DSS na sane da yadda wasu miyagu ke son tayar da rikici a kasar nan, gami da haifar da cece-kuce game da babban zabe mai zuwa.

“Kuma wannan na daya daga cikin dabarun su na yin zagon kasa da lalata kokarinmu na tabbatar da zaman lafiya da kwanciyar hankali a Najeriya.


“Don haka ina amfani da wannan dama, don wanke DSS da kuma fahimtar da al’umma cewa, ba gaskiya ba ne cewa mun kai karar shugaban INEC kotu”, in ji Kakakin.

Ana shirin mayar da tubabbun mayaƙan Boko Haram 613 cikin al'umma

Hukumomi a Najeriya sun kammala shirin miƙa wasu mayaƙan Boko Haram fiye da 600 da suka tuba ga gwamnatocin jihohinsu domin shigar da su cikin sauran al`umma.

Hedikwatar tsaron Najeriyar ta bayyana cewa an ɗauki wannan matakin ne bayan an shigar da su cikin wani shirin gyara hali.

 BBC Hausa ta rawaito Hafsan hafsoshin Najeriya, Janar Lucky Irabor ya bayyana cewa an kammala shirin miƙa mayakan Boko Haram ɗin da suka tuba su 613, bayan an gyara musu hali.

Ya yi bayanin ne a wajen wani taron masu hannu ko ruwa da tsaki a ƙarƙashin tsarin nan na ba da damar miƙa wuya ko tuba ga mayaƙan Boko Haram, wato Operation Safe Corridor.

Ya ce za a mika su ne ga jihohinsu na asali domin shigar da su cikin al`umma, kuma a halin da ake ciki ana gab da kammala aikin sauya musu tunani da zare musu tsattsaurar akida.

 A cewar Hafsan hafsoshin, tubabbun mayakan Boko Haram ɗin na bukatar kulawa sosai a wannan gaɓa ta gyara hali da sake shiga cikin jama`a, don haka sai jihohin sun tsaya sosai a kan su.

Batun gyara hali aikin ne jawur, saboda ko a nasu matakin sai da suka haɗa da kwararru daga fannoni daban-daban, da ma'aikatu da hukumomin gwamnati masu yawa, da kuma taimakon kungiyoyin agaji na kasa da kasa.

Ya ce za yi nasarar shigar da tsoffin mayakan cikin al'umma idan jihohi suka yi tsari mai kyau, tare da haɗa gwiwa da sarakunan gargajiya wajen sa-ido a kan tubabbun yayin da suke sajewa a cikin al'umma.

Janar Irabor ya ce idan aka zo sallama ko yaye tsoffin ƴan Boko Haram din, za a ba su guzurin kayan abinci da kayan zaman gida da kuma kayan aiki irin sana'ar da suka koya don fuskantar gangariyar rayuwa.

Game da yakin da ake yi da kungiyar Boko Haram kuwa, Hafsan hafsoshin ya ce askarawan gwamnati na samuN nasara a kan su, kuma da dama sai mika wuya suke yi sakamakon mamayar dajin Sambisa da zaratan sojojin suka yi da fatattakar su da ake yi inda ta kai ga fiye da mayakan Boko Haram da iyalansu 80,000 sun mika wuya.


Yan sanda a jihar Kano sun kame 'yan daban siyasa fiye da 60

‘Yan sanda a jihar Kano sun sanar da kame ‘yan daban siyasa akalla 61 yayin wani sumame da suka kaddamar a kokarin kakkabe barazanar rashin tsaro da aikata laifukan da ke ci gaba da tsananta a sassan jihar.

Kwamishinan ‘yan sandan jihar Mr Mamman Dauda da ke bayyana hakan a wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Abdullahi Haruna ya rabawa manema labarai, ya ce matakin kame ‘yan daban umarni ne daga babban sufeton ‘yan sandan kasar Usman Alkali-Baba.

A cewar sanarwar galibin kamen an yi shi ne yayin gangamin siyasar da ke ci gaba da gudana a sassan jihar, a wani yunkuri na dakile barazanar ‘yan daban dai dai lokacin da babban zaben Najeriya ke ci gaba da karatowa.

A Sanarwar da gidan Rediyon Faransa (RFI) ya wallafa a shafinsa, ta bayyana cewa ta hanyar tsaftace gari daga barazanar ‘yan daban siyasa ne kadai za a iya samun damar tafiyar da harkokin zaben da ke tunakarowa a wata mai zuwa.

Rundunar ‘yan sandan ta jihar Kano ta ce ta gudanar da sumame ranar 4 ga watan da muke na Janairu yayin wani gangamin siyasa da ya gudana a filin wasa na Sani Abacha da ke jihar.

Sanarwar ‘yan sandan ta ce ta kame tarin makamai daga hannun ‘yan daban da suka kunshi wukake 33 da adda guda 8 da almakashi 4 baya ga kunshin tabar wiwi 117.

Jihohin Najeriya na neman Majalisar wakilai ta sa su cikin harkar samar da wuta

Kwamitin majalisar wakilan Najeriya da ke kula da harkokin wutar lantarki ya yi zama don jin ra'ayin jama'a, game da wani garambawul da majalisar ke shirin yi ga dokar lantarki domin bai wa jihohi damar shiga harkar samar da wuta.


Kwamitin ya ɗauki matakin ne bayan da jihohi suka nemi a basu damar shiga harkar a matakai daban-daban, da suka haɗa da samarwa da kuma rarrabawa.


Mahukunta a Najeriya dai sun sha nuna rashin gamsuwa da yadda kamfanonin wutar lantarkin suke gudanar da harkokinsu.


Honourable Magaji Ɗa'u Aliyu, shugaban kwamitin ya shaida wa BBC cewa "akwai kamfanin da ke ruwa da tsaki wajen tafiyar da harkokin wutar lantarki a ƙasar, sai dai ya ce jihohi a yanzu sun nemi a basu dama "su je su yi nasu".


"Mun saurare su, kuma sun kawo mana kundin da suka yi aiki a kai, za mu duba shi sannan kuma za mu faɗa musu halin da ake ciki a kai."

A cewarsa, gaba ɗaya jihohin Najeriya sun sa hannu a takardar da aka miƙa musu "har sun aiko da wakilai daga jihohi guda shida."shida.

Ban da gwamnatocin jihohi, ƙungiyoyi da wasu ɗaiɗaikun jama'a su ma sun bayyana nasu ra'ayin, kuma mafi yawa na nuna goyon baya ga yunƙurin da majalisar ke yi na gyaran fuska ga dokar wutar lantarkin.

Ita ma gwamnatin Najeriya a nata ɓangaren ta ce ta yi na'am da maganar garambawul ɗin sosai sakamakon rashin gamsuwar da ta yi da takun kamfanonin da aka damƙa wa samar da wutar lantarkin a halin da ake ciki.

Minista a ma'aikatar wutar lantarki a Najeriya, Mista Goddy Jedy Agba, ya bayyana cewa yin gyaran na da muhimmanci ga al'ummar ƙasar.

"Muna son gyaran, kowa na son wuta a Najeriya, idan an yi aikin sai mu samu ci gaba."

Ya ce akwai matakai na samar da wutar lantarki - samarwa da rarrabawa kuma a halin da ake ciki, gwamnati kawai tana samar da wutar ne kawai.

"A wannan shekara, za mu cire hannu daga samarwa, zai zama kowa zai taka rawa"

Kwamitin wutar lantarkin dai ya ce zai miƙa bayanan da ya tattara ga zauren majalisar wakilai, kuma a can ne za a yi tankaɗe da rairaya gabanin yanke shawara a kan abin yi.

Batun inganta wutar lantarki daɗaɗɗiyar magana ce a Najeriya, da aka yi yunƙuri daban-daban tun gabanin komawar ƙasar ga dimokraɗiyya, aka kuma ci gaba da kwan-gaba-kwan-baya har zuwa yau.

Kodayake za a iya cewa wutar da ake samarwa ta ƙaru a tsukin nan, amma kuma a ɓangare guda, ƴan ƙasar na kukan cewa ta yi ɗan karen tsada.

An haramta cire tsabar kudi daga asusun Gwamnati

Hukumar da ke sanya ido kan hada-hadar kudade a Najeriya (NFIU) ta haramta cire tsabar kudi daga asusun Gwamnatin Tarayya da jihohi da kuma kananan hukumomi daga ranar 1 ga watan Maris, 2023.

NFIU ta ce daga ranar, laifi ne a biyan ma’aikatan gwamnati alawus-alawus din tafiyar aiki a cikin gida ko zuwa kasashen waje da tsabar kudi.

An gano gawar mutum 16 a hatsarin jirgi a Kebbi
’Yan sanda sun cafke ’yan daba 63 a taron Tinubu a Kano
Babban Daraktan hukumar, Modibbo Tukur, ne ya bayyana haka a Abuja ranar alhamis, inda ya ce karin wasu sabbin tsare-tsaren na tafe.

Ya ce za a fara amfani da sabbin tsare-tsaren ne bayan fara aikinsa dokar Babban Bankin Najeriya (CBN) na takaita cirar tsabar kudi ga daidaikun mutane da kamfanoni a Najeriya.


Da yake karin haske kan dokokin, Modibbo ya ce hakan yayi daidai da sashi na 3(1)a-s, da sashi na 23(2) na kundin hukumar.

A baya dai bisa dalilai daban-daban, ma’aikatun gwamnati da hukumomi, na fitar da kudade daga bankuna don yin mu’amalar kasuwanci a hukumance da ba a iya ganowa cikin sauki, maimakon ta hanyar musayar bankuna.

Thursday, 5 January 2023

Gwamnatin Soja ta fi ta farar hula tausayin malaman Jami'a - ASUU

Shugaban Kungiyar Malaman Jami’o’i ta Kasa (ASUU), Farfesa Emmanuel Osodeke, ya ce gwamnatocin mulkin soja na baya a Najeriya sun fi ta farar hula mai ci a yanzu tausayin su.

Ya bayyana haka ne ranar Alhamis a Abuja, yayin kaddamar da wasu littattafan manyan makarantu guda 50 da wasu marubuta suka wallafa.

Hukumar da ke Kula da Manyan Makarantu ta Najeriya (TETFund), ce dai ta dauki nauyin wallafa littatafan.

A cewar Shugaban, “A shekarar 1992, lokacin da muka yi yajin aiki, sai muka bukaci a kalubalance mu, mu kawo mafita kan yadda za a samo kudaden da za a aiwatar da yarjejeniyoyin da aka amince da su.


“Haka aka yi kuwa suka kalubalanci ASUU, inda ko kwana uku ba a yi ba muka kawo batun kafa TETFund, wacce kuma gwamantin mulkin soja ta wancan lokacin ta amince. Ni ina ga gwamnatin soja ta ma fi ta farar hula tausayinmu.

“Yadda aka yi aka sami hukumar TETFund ke nan. An rattaba hannu a kan kudurin ya zama doka a 1993. Sai da ASUU ta sake komawa yajin aiki a karo na uku kafin a fara fitar wa TETFund kudi,” inji Shugaban na ASUU.
Dangane da matakin “babu aiki babu albashi” na Gwamnatin Tarayya da ya kai ga malaman suka shafe wata takwas suna yajin aiki a bara kuwa, Farfesa Emmanuel Osodeke ya roki ’yan Najeriya da su dada matsa wa gwamnati lamba ta ceto manyan makarantun kasar daga durkushewa.

Shi ma da yake jawabi yayin kaddamar da littattafan guda 50, Ministan Ilimi, Malam Adamu Adamu, ya ce sabbin littattafan za su rage kaka-gidan da na ketare ke yi a manyan makarantun kasar.


Adamu, wanda Minista a Ma’aikatar Ilimi, Goodluck Nanah Opiah ya wakilta, ya ce an yi lokacin da kusan dukkan makarantun Najeriya suka ta’allaka da na ketare, duk kuwa da makudan kudaden da ake kashewa wajen musayar kudade kafin sayo littattafan.


An sanyawa Jarirai fiye da Dari 700 sunan Pele a Peru

Hukumar Kididdigar Kasar Peru ta bayyana cewar a yayin da duniya ke alhinin rasa Pele, gwarzon dan kwallon kafa na karni, sunansa zai rayu a tsakanin yara fiye da 700 ‘yan kasar da aka haifa a karshen shekarar 2022.

Jerin sunayen da jami’an kasar ta Peru suka fitar ya nuna cewar, bayan mutuwarsa gwarzon dan kwallon kafar, an rada wa jarirai 738 da aka yi wa rajista a hukumance sunan ko dai Pele, ko King Pele, ko kuma Edson Arantes ko Edson Arantes do Nascimento, cikakken sunan zakaran kwallon kafa na duniya sau uku.

A ranar 29 ga watan Disamba Pele ya mutu yana da shekaru 82 a duniya, wanda kuma aka binne shi a ranar Talata.

Iyayen yara a kasar Peru dai sun saba rada wa ‘ya’yansu sunayen fitattun mutane da suke kauna walau a cikin ‘yan wasa ko kuma shugabanni kamar yadda RFI ya ruwaito.


Wata kididdiga ta nuna cewar a yanzu haka, sunan Cristiano Ronaldo ne aka fi rada wa yaran kasar, wadanda adadinsu ya kai dubu 31 da 538.

Messi kuwa na da takwarori jarirai 371 ne a baya bayan nan a kasar ta Peru, wadanda ko dai aka sanya musu suna Leo Messi, ko Messi kadai bayan da ya lashe Gasar Kofin Duniya.

Yarima Harry na Burtaniya ya zargi yayansa Yarima Williams da dukansa

Yarima Harry ya yi da'awar cewar yayansa Yarima William ya taɓa dukan sa, in ji jaridar Guardian, wadda ta ce ta ga wani ɓangare na littafin da yarima Harry ɗin ke rubutawa, mai taken 'Spare'.

Jaridar ta ruwaito cewa littafin ya ambato wani lokaci da aka samu sa-in-sa tsakanin ƴan'uwan biyu a kan matar Harry, Meghan.

Jaridar ta ce a cikin littafin Harry ya rubuta cewa "ya ci kwalata, ya tsinka sarƙar da ke wuyana, sannan ya bugani da ƙasa."

Sai dai Majiyarmu ba ta kai ga ganin littafin na 'Spare' ba.

Ba za a buga littafin ba sai ranar Talata ta sama, amma jaridar Guardian ta ce ta ga littafin a wani abu da ta kira " bugun kafin a wallafa".

Kawo yanzu fadar Buckingham ba ta ce komai ba, duk da cewa an tuntuɓe ta kan batun.bayar da rahoto kan lamarin, ba mu kira shi da faɗa ba, saboda Harry bai mayar da martani ba.

A cewar jaridar Guardian "Yarima Harry ya rubuta cewar ɗan uwansa ya nemi da ya rama bugun da ya yi masa, amma ya ƙi, sai dai daga baya Yarima William ya yi "nadama, ya kuma ba shi haƙuri".
Hotuna sun nuna yadda Yarima Harry ke sanya baƙar sarƙa, a taro irin na wasannin Invictus, da lokacin tafiya zuwa wata ƙasa shi da Meghan, kamar yadda suka yi a watan Satumbar 2019.

Har yanzu kamfanin wallafa littatafai na Penguin Random bai kai ga tabbatar da cewar ko wadancan bayanai da suka fita daga littafin, kan batun da Yarima Harry ya yi cewar yana da saɓani da ɗan uwansa, gaskiya ne ko kuwa akasin haka ba.

A wani fim na rayuwar Harry da Meghan na Netflix, Yarima Harry ya bayyana taron da ya halarta da ɗan uwansa, da mahaifinsa da yanzu ya zama sarki.

Yarima Harry ya bayyana taron farkon shekarar 2020, wanda marigayiya sarauniyar Ingila ta hallarta, da "abin kaɗuwa".

Yarima Harry ya ce "abin kaɗuwa ne, da na ji yayana na ihu da ɗaga murya gare ni, da mahaifina, yana faɗar abubuwa da babu gaskiya a cikinsu, kakata na zaune ta yi shiru tana jin abin da ke faruwa,".

Jaridar Guardian ta ce, Prince Harry ya bayar da cikakkun bayanai kan yadda zamansu ya kasance da Sarki Charles, a lokacin yana Yariman Wales, da Yarima William bayan jana'izar kakansa Yarima Phillip, a Afrelun 2021.

A cewar jaridar, Yarima Harry ya rubuta cewar, mahaifinsa ya shiga tsakaninsu shi da Yarima Williams, yana cewar "don Allah yara kar ku sa shekaruna na ƙarshe su kasance cikin ƙunci".

A wata hira da za a haska a ranar 8 ga watan Janairu, kafin sakin littafin, yariman ya ce: "Zan so na daidaita dangantakata da mahaifina da ɗan'uwana".

Ko da yake Yarima Harry ya shaida wa Tom Bradby na tashar ITV cewar, ba su nuna sha'awarsu ta son a daidaita ba," duk da cewar ba a fahimci taƙamaimai wa yake nufi ba.

Ko da aka tuntuɓi fadar Buckingham kan lamarin, ta ƙi cewa komai a kai.

A wani jawabi da kamfanin wallafa litattafai na Penguin Random ya yi a watan Octoban bara, ya ce "daga ƙarshe - wannan shi ne labarin Harry".

"Da irin tsagwaron gaskiyar da ke cikin littafin Spare, littafi ne da ke cike da bayanai, da tone-tone, da fadin ra'ayin kai, da darusan da ya koya kan mulki da soyyaya kan baƙin ciki.

Mutum miliyan bakwai ne suka yi aikin Umarah a shekarar 2022- Saudia

Ma’aikatar Aikin Hajji da Umarah ta kasar Saudiyya ta ce kimanin mutum miliyan bakwai ne suka yi aikin Umarah a shekarar 2022.

Jaridar Aminiya ta rawaito cewa wannan adadin a cewar ma’aikatar ya hada da baki su miliyan hudun da suka samu izinin shiga kasar domin Hajjin Umarah.

Kamfanin dillancin labarai na SPA ya rawaito a ranar Alhamis cewar, Ma’aikatar ta yi amfani da harsuna 14 wajen isar da muhiman bayanai da suka shafi addini da kiwon lafiya da sauransu ga maniyyatan yayin zamansu a kasar.

Kazalika, ta ce ta tabbatar da maniyyatan sun samu kulawar da ta dace wajen gudanar da harkokinsu da suka hada yanka da ziyartar wurare da sauransu.

Ta kara da cewa, ta sahale wa masu rike da biza daban-daban ibadar Umarah a wannan shekarar.

Ta ce a 2022 ne ta kyale masu bizar yawon shakatawa suka yi Umarah yayin zamansu a kasar, wanda hakan shi ne karon farko da irin hakan ta faru.


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Presidential delegation pays condolence visit to Hamza Darma’s family in Kano

A high-powered presidential delegation has paid a condolence visit to the family of late Alhaji Hamza Usman Darma, a prominent K...