Search This Blog

Tuesday, 3 January 2023

Gwamnatin Tarayya Da Gwamnonin 36 Sun Shiga Yarjejiniyar Sayar da Kamfanonin Wuta 5

 


A wata sanarwa da darekta janar na ofishin sayar da kaddarorin gwamnati wato BPE Alex Okoh ya fitar, ya nuna cewa za a sayar da kamfanonin wuta biyar a kwatan farko na wannan shekara da muka shiga, domin samar da kudade da za a cike gibin Kasafin kudin shekara 2023 da su.

Kasafin kudin na Naira Triliyan 21.82 ya zo da gibi har na kusan Naira triliyan 11 saboda rashin kudin shiga, haka ya sa aka samu gibin kashi 4.8 a ma'unin arzikin kasar wato GDP, wani abu da masanin tattalin arziki na kasa da kasa Shuaibu Idris Mikati ya nuna damuwa akan batun sayar da kamfanonin yana cewa akwai abin dubawa a wannan batun sayar da kamfanonin nan domin kar a sake fadawa cikin halin kakanakayi.

  • https://alheekmah.blogspot.com/2023/01/labari-da-dumiduminsa-yusuf-babangida.html
  • https://alheekmah.blogspot.com/2023/01/obasanjo-ya-zama-tamkar-dan-bakin-ciki.html

Mikati ya ce haka aka sayar da kamfanoni ga wadanda ba su da kudi a zamanin gwamnatin da ta shude, har suka gagara ba kasa wadataccen wuta. Mikati ya ce ya yi mamakin wai bankin UBA ne za sayar wa da kashi 60 na kamfanonin inda ya kira da a duba lamarin da idanun basira.

Kamfanonin da ke samar da wutan lantarki ( GENKOS) wadanda za a sayar sun hada da tashar wutar lantarki ta Geregu, da cibiyar samar da wutar lantarki mai karfin megawatt 562 a Calabar Jihar Kros Ribas da kuma cibiyar wutar lantarki ta Olorunsogo, amma ga mai fashin baki a al'amuran zamantakewa da gudanar da mulki Dokta Abdulrahaman Abu Hamisu ya ce wannan ya zo masa da mamaki domin ya kamata Najeriya ta yi damokradiya da gaske.

Abu ya ce matakin da ake dauka bai dace ba domin yana ba sai an sayar da kaddarori kafin a cike gibin kasafin kudi ba.

Abu ya ce ya kamata Najeriya ta yi koyi da wasu kasashe da suka cigaba wajen karban haraji maimakon sayar da kaddarori. Abu ya koka da yadda ake sace kudaden kasa ba tare da an kamo barayin ba. Ya kara de cewa idan ba a hanzarta samo hanyoyin kudaden shigowa ba, to da sauran rina a kaba, musamman yanzu da ake shirin zaben sabon gwamnati.

To sai dai ga tsohon mai ba ministan makamashi shawara a harkar gudanarwa, Idris Mohammed Madakin Jen yana mai ganin an dauki mataki mai kyau da zai kawo wa kasa wutar lantarki.

Idris ya ce dama kudaden na jihohi da kananan hukumomi ne, kuma lokaci ya yi da za a basu abinsu. Idris ya ce bankin UBA ce ta samo masu hannu da shuni da za su saye kamfanin samar da wutan lantarki musamman na birnin taraiyya Abuja.

Majalisar kula da harkokin kasuwanci ta kasa NCP ta amince da tsarin gudanar da aikin gina wani katafaren kamfani na dalar Amurka biliyan 3 da zai samar da wutan lantarki mafi girma a Afirka ta Yamma.

VOA

Monday, 2 January 2023

LABARI DA DUMIDUMINSA: Yusuf Babangida (Dawo-dawo) ya raba gari da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso

Dan majalisar Jaha mai wakiltar yankin karamar hukumar Gwale, Yusuf Babangida (Dawo-dawo) ya raba gari da Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso, ya dawo Jam'iyyar #APC 

📷 Mai taimakawa Gwamna na musamman kan harkokin daukar Hoto (Aminu Dahiru Ahmad) 

Obasanjo ya zama tamkar dan bakin ciki - Fadar Shugaban kasa

Fadar Shugaban Najeriya ta mayar da kakkausan martani kan kalaman da Tsohon Shugaban Najeriya Olusegun Obasanjo ya yi a saƙonsa na sabuwar shekara.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Najeriya Malam Garba Shehu ya fitar, sanarwar ta ce Obasanjo ba zai taɓa daina caccakar Shugaba Muhammadu Buhari ba sakamakon Obasanjon ba zai daina baƙin ciki kan duk wani wanda ya sha gabansa a ayyukan ci gaban ƙasa ba.

Fadar shugaban ƙasar ta buga misali da cewa Shugaba Buhari ya kammala gadar Neja ta biyu bayan an yi shekara 30 ana alƙawura a kanta.

Haka kuma fadar shugaban ƙasar ta ce Obasanjo ya yi wa kudu maso gabashin Najeriya ƙarya domin ya samu ƙuri'unsu, amma Shugaba Buhari bai samu ƙuri'unsu ba amma duk da haka sai da ya yi musu aikin gadar.

Fadar shugaban ƙasar ta kuma ce Obasanjo yana baƙin ciki ne sakamakon yana ganin yadda Buhari ke samun lambobin yabo da kuma yadda shugaban ke ci gaba da da'awar cewa zai tabbatar an gudanar da sahihin zaɓe fiye da wanda ya kawo sa kan karagar mulki.

Haka kuma fadar ta zargi Obasanjo da lalata dimokraɗiyya a Najeriya bayan kitsa tsige wasu gwamnoni a ƙasar da suka haɗa da Joshua Dariye da Rashidi Ladoja da Peter Obi da Chris Ngige da Ayo Fayose.

Wannan martanin na fadar shugaban Najeriya duk na zuwa ne bayan tsohon Shugaban Najeriyar Chief Olusegun Obasanjo ya ce Peter Obi ne zaɓinsa a zaɓen 2023 haka kuma Obasanjon ya caccaki gwamnatin Shugaba Buhari

Obasanjo ba zai iya kawo mazabarsa ba - Tinubu


Dan takarar shugaban kasa na Jam’iyyar APC, Bola Ahmed Tinubu, ya gargadi Peter Obi, cewa kada ya rudu da goyon bayansa da tsohon shugaban kasar Najeriya, Olusegun Obasanjo ke yi.

Tinubu ya ce goyon bayan Obasanjo ba zai kai Peter Obi ko’ina ba, saboda Obasanjo ba zai iya lashe akwatin mazabarsa ba.

“Bincikenmu mun gano Obasanjo bai taba nasarar sa wani ya lashe kujerar shugaban kasar Najeriya ba.

“Ko a Jihar Ogun babu wanda zai dogara da shi don lashe kujerar gwamna ko kansila,” in ji Tinubu  ta hnnun Daraktan yada labarai na kwamitin yakin neman zaben Tibubu, Bayo Onanuga.

Ya ci gaba da cewa, “Muna tausaya wa Peter Obi domin Obasanjo ba zai iya lashe masa akwatin mazabarsa da ke Abeokuta ba a zaben ranar 25 ga watan Fabrairun 2023.”

Tsohon gwamnan na Legas, ya bayyana yadda Obasanjo ya goyi bayan tsohon mataimakinsa, Atiku Abubakar a zaben 2019 kuma ya sha kaye a hannun Shugaba Buhari.

Tinubu ya jadadda cewa da taimakonsa Buhari ya samu gagarumar nasara a zaben tare da tika Atiku da kasa.

Ya ce tarihi ne zai sake maimaita kan sa a zaben da ke kara kartowa a watan Fabrairu.


Rasha ta ce, an kashe mata sojoji 63


Rasha ta ce, an kashe mata sojoji 63 a wani kazamin hari da Ukraine ta kaddamar kan dakarunta a karshen makon da aka gudanar da bukukuwan shiga sabuwar shekara.

A cikin wata sanarwa da ba a saba ganin irinta, Ma’aikatar Tsaron Rasha ta ce, an kashe sojojin kasar 63 sakamakon wani harin makami mai linzami da Ukraine ta kaddamar kan birnin Makiivka da ke gabashin Ukraine wanda Moscow ta mamaye.

Wannan ne asarar sojoji mafi girma da Rasha ta yi tun bayan barkewar yaki tsakaninta da Uktraine a ranar 24 ga watan Fabairun da ya gabata.

Rasha ta ce, an yi amfani da shu’umin na’urar cilla makaman roka da aka kera a Amurka wajen kaddamar mata da wannan farmakin, yayin da a Babban Hafsan sojin Ukraine ke cewa, dakarunsu ne suka kai harin a Makiivka.

Ya kara daa cewa, sun lalata wuraren ajiyar makaman Rasha har guda 10 a yayin harin.

Tun da fari, Sashen Yada Labarai na Rundunar Sojin Ukraine ya yi ikirarin cewa, kimanin sojojin Rasha 400 ne suka mutu a Makiivka sabanin 63 da aka ba da rahoto.

An sace gangan man fetur miliyan 17 a Najeriya

 


Wani sabon bincike da aka gudanar kan lamurran da ke wakana a fannin arzikin man Najeriya ya nuna cewar, an fitar da ganga sama da miliyan 17 na danyen mai daga kasar zuwa kasashen ketare ta barauniyar hanya, a tsakanin shekarar 2016 zuwa 2020.

Rahoton da Andrew Ogochukwu Onwudili, babban jami’i mai binciken kudi na Najeriya ya fitar, wanda kuma jaridar The Nation da ke kasar ta ruwaito, ya kiyasta cewarkwatankwacin kudin danyan man fetur din da a iya cewa an sace daga kasar ya kai Dala Tiriliyan 1 da biliyan 20, da miliyan 969 da dubu 281.

A cikin rahoton, an tuhumi  Ofishin Akanta-Janar na gwamnatin Najeriya da laifin biyan sama da Naira biliyan 73 ga jami’an da suke tantance inganci da adadin albarkatun mai da isakar gas din da ake shirin fitar da su daga kasar.

Mai binciken yadda ake kashe kudaden Najeriyar ya bayyana cewar, kudaden da aka biya ba tare da an yi  kasafinsu ba, ya saba wa tanadin doka a sashi na 80(4) na kundin tsarin mulkin kasar na shekarar 1999.

Tsohon babban mai binciken kudi, Adolphus Agughu ne ya sanya hannu kan rahoton, aka kuma mika kundin ga magatakardar majalisar dokokin Najeriya a ranar 29 ga Yuni, na shekarar da ta gabata.

RFI

Kotun Senegal ta daure 'yan majalisa saboda dukan mace

 


Kotu a Senegal ta yanke hukuncin daurin watanni 6 a kan ‘yan majalisar dokokin kasar su biyu na bangaren 'yan adawa, saboda samun su da laifin dukar abokiyar aikinsu daga bangaren masu rinjaye.

A ranar 1 ga watan Disambar da ya gabata ne dan majalisar dokoki Massata Samb ya yi dirar mikiya a kan wata ‘yar majalisar mai suna Amy Ndiaye, bisa zargin furta kalaman batanci a kan Moustapha Sy, shugaban wata jam’iyyar siyasa da ke cikin gungun ‘yan adawa sannan kuma shehin malamin addinin musulunci da ake mutuntawa a kasar.

Wasu hotuna da ake rika yadawa sun nuna yadda Massata Samb ya lafta wa Amy Sy mari a cikin zauren majaliar ‘yayin da abokinsa dan majalisa Mamadou Niang ya sa kafa ya noshi matar a ciki bainar jama’a.

Bayan faruwar wannan lamari, an kwantar da ‘yar majalisa Amy Sy a asibiti bayan da bayanai suka tabbatar da cewa tana dauke da juna biyu a lokacin faruwar lamarin, to sai dai a lokacin da yake yanke hukunci, alkali ya yi watsi da zargin yunkurin kisa kamar dai yadda masu shigar da kara suka bukata.

Ko baya ga hukuncin dauri, hakazalika kotun ta bukaci mutanen biyu su biya tarar cfa jika dari a matsayin diyya saboda dukar da suka yi wa ‘yar majalisar wadda ta fito daga jam’iyyar shugaba Macky Sall.

’Yan Bindiga Sun Sace Tsohon Kanar Din Soja A Zamfara

 


’Yan bindiga sun sace Kanar Lawal Rabiu Yandoto (mai ritaya) a kan hanyarsa ta zuwa garinsu, Yandoto da ke Karamar Hukumar Tsafe a Jihar Zamfara.

Wata majiya ta bayyana cewa ’yan bindigar sun sace shi ne tare da ’ya’yansa biyu da kuma wasu.

“Maharan sun yi wa Kanar kwanton bauna da misalin karfe 6 na yamamcin ranar Lahadi, suka sace shi tare da ’ya’yansa biyu da kuma wasu mutum biyu,”  in ji majiyar.

Majiyar ta ce an ji karar harbe-harbe daura da shiga garin na Yandoto lamarin da ya tilasta mutane guje-guje domin tsira.

Kakakin ’yan sandan jihar bai daga waya ba ballatana a ji ta bakinsa kan lamarin.

(AMINIYA)

Masu Sukar Lafiyata Ba Su Da Abin Yi Ne —Tinubu


Dan takarar Shugaban Kasa na jam’iyyar APC, Bola Ahmad Tinubu, ya ce sukar lafiyarsa da wasu ke yi shirme ne tsagwaronsa.

Da yake zantawa da Tashar Freedom Radio ta Kano a Saudiyya, Tinubu ya ce ya yi Dawafi inda ya kewaye Ka’abah sau bakwai ya kuma yi Safa da Marwa wanda mara lafiya ba zai iya aikata hakan ba.

Masu sukar Tinubu sun dage da kira kan cewa dan takarar ba zai iya rike Najeriya ba saboda rashin koshin lafiya.

Sai dai Yinubun ya ce masu korafi game da lafiyarsa shirme ne kawai, saboda “Yanzu na kammala aikin Umarah, na yi Dawafi sau bakwai da Safa da Marwa da kaina.

“Kwarai ga ni a Saudiyya, bukatar kaina ta kawo ni. Tun fil azal ni mai sha’awar yin Umarah ne saboda dama ce ta ganawa da Ubamgiji,” in ji Tinubu.

Game da batun halartar tarurrukar tattaunawa da jama’a, Tinubu ya ce masu korafin ba a ganin shi a wajen tarurrukan wadanda suka sha kaye ne kuma haka za su ci gaba da shan kaye.

(AMINIYA)

Ya ce a saninsa yana zagayawa don tattaunawa da jama’a walau kai tsaye ko kuma bisa wakilci.

Sunday, 1 January 2023

Mun Kama Bako Da Kullin Hodar Iblis 105 Daga Brazil —NDLEA



Hukumar Yaki da Sha da Fataucin Miyagun Kwayoyi ta Kasa (NDLEA) ta kama kullin hodar iblis 105 a cikin kayan wani wanda ya dawo daga kasar Brazil a Babban Jirgin Sama na Murtala Mohammed da ke Legas.

Daraktan yada labarai na hukumar, Femi Babafemi, ya sanar ranar Lahadi a Abuja cewa sun kama wanda ake zargin ne ranar Kirsimeti.

Ya ce wanda ake zargin na daga cikin fasinjojin da suka dawo daga birnin Sao Paulo na kasar Brazil.

A cewarsa, bayanan sirrin da suka samu sun taimaka wajen kama wanda ake zargin a filin jirgin.

Da aka tsananta bincike a kansa karo na biyu, sai aka gano hodar iblis din da yake dauke da ita, in ji jami’in.

Shugaban NDLEA na Kasa, Birgediya-Janar Buba Marwa (Murabus), ya sha nanata cewa ba za su raga wa masu fataucin miyagun kwayoyi ba ko’ina suke a fadin kasa.

(AMINIYA)

(NAN)

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Presidential delegation pays condolence visit to Hamza Darma’s family in Kano

A high-powered presidential delegation has paid a condolence visit to the family of late Alhaji Hamza Usman Darma, a prominent K...