Search This Blog

Saturday, 6 May 2023

Hukumar Lafiya ta Duniya ta ayyana karshen annobar Covid-19

A jiya Juma’a ce hukumar Lafiya ta Duniya ta ce an kawo karshen annobar Covid-19, wadda ta yi sanadin mutuwar mutane da dama tare da wargaza tattalin arziki da sha’anin zamantakewar duniya, sama da shekaru 3 bayan da ta ayyana ta a matsayin annoba. 

Shugaban hukumar Tedros Adhanom Ghebreyesus ne ya sanar da haka a jiya Juma’a, inda ya yi gargadin cewa har yanzu cutar na nan a matsayin barazana.

Wannan mataki na hukumar Lafiyar na zuwa ne bayan da kwamitin kwararru mai zaman kansa da ta nada a game da wannan cuta ta Covid ya ce cutar ba a bukatar mayar da hankali sosai a kan cutar daga hukumar.

Sai dai a cewar Tedros, hatsarin cutar bai kau ba, inda ya yi kiyasin cewa ta kashe sama da mutane miliyan 20 a fadin duniya, kimanin ninki 3 na mutane kusan miliyan 7 da aka ce ta kashe a hukumance.

A ranar 30 ga watan Janairun shekarar 2020 ce hukumar Lafiya ta Duniya ta ayyana cutar Covid-19 a matsayin annoba, makwanni bayan da ta bulla a birnin Wuhan na kasar China.
RFI 

Zaben Adamawa: An Ba Da Belin Kwamishina Hudu

 


’Yan sanda sun bayar da belin Kwamishinan Zabe na Jihar Adamawa da aka dakatar, Hudu Yunusa-Ari, bayan da ya yi kwana uku a tsare a hannunsu.

’Yan sanda sun cafke shi ne kan wata sanarwa mai cike da rudani da ya yi  cewa Sanata Aisha Dahiru Binani ta lashe zaben gwamnan jihar Adamawa, alhali ba a kammala karbar sakamakon karashen zaben ba.

Tun a lokacin INEC ta soke sanarwar, sannan ta bukaci ya gabatar da kansa a hedikwatarta da ke Abuja, amma maimakon ya je, sai ya yi layar zana.

Daga bisani hukumar ta rubuta Shugaban ’Yan Sandan Najeriya wasikar neman ya binciki kwamishinan zaben, kan yamutsa hazon da ya yi.

Amma wata wasika da ya aike wa shugaban ’yan sanda, Hudu ya ce ya yi sanarwar ne a bisa doka, saboda dalilan tsaro.

A ranar Talala ’yan sanda suka sanar cewa sun kama Hudu, wanda ya ce ba ya nadamar sanarwar da ya ya yi cewa Binani ta ci zabe.

Amma kakakin rundunar ’yan sandan Najeriya, Muyiwa Adejobi, ya sanar a ranar Juma’a cewa rundunar ta bayar da belin kwamishinan zaben.

Muyiwa ya cen an umarci Hudu ya rika zuwa hedikwatar rundunar a ranakun aiki domin ci gaba da binciken da ake gudarwa.

AMINIYA

Friday, 5 May 2023

#Hajj2023: Shugaba Buhari Ya Amince Da Cire Kaso 65 Na Kudaden Haraji Da Kamfanonin Jirage Ke Biya

A ci gaba da shirye-shiryen gudanar da aikin Hajjin shekarar 2023, Hukumar Alhazai ta kasa NAHCON ta gana da masu ruwa da tsaki a harkar sufurin jiragen sama a dakin taro na Hajj House dake Abuja. 

A sanarwar da Mataimakiyar Daraktar harkokin hulda da jama’a ta hukumar NAHCON, Hajj2023 Hajiya Fatima Sanda Usara ta fitar, tace an yi hakan ne domin inganta shirye-shiryen da suka kasance masu tasiri wajen jigilar maniyyata Hajji.
 
A taron shirye-shiryen kulla yarjejeniyar jigilar alhaza tare da masu jigilar kayayyaki da aka zaba, Alhaji Zikrullah Kunle Hassan ya bayyana matakan da hukumar ta riga ta dauka na dakile cikas da za a iya samu da zarar an fara jigilar Alhazan 

Shugaban NAHCON ya yi albishir da cewa shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da rage kashi 65 cikin 100 na kudaden sufurin jiragen sama na jiragen sama.
 
Ya kuma sanar da cewa, domin tabbatar da an samar da man jirgi a wadace don jigilar alhazai , NAHCON ta yi shiri da Kamfanin Mai na Najeriya (NNPC) domin kawo karshen hakan. An shawarci masu jigilar maniyyatan da su gana da NNPC da nufin tattaunawa don gujewa matsala 

A cewar shugaban hukumar ta kuma tuntubi masana harkokin sufurin jiragen sama don samun shawarwarin kwararru kuma hukumar za ta ci gaba da bin shawarwarin domin amfanin alhazan Najeriya da kuma kare lafiyar alhazan baki daya 
 
Darakta Janar na Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama ta Najeriya (NCAA), Kyaftin Musa Nuhu wanda ya halarci taron ya bayyana cewa, hukumar tasu ta duba dukkan filayen saukar jiragen sama na Hajji da aka tanada domin samar da tsaro da kayan aiki. Ya yi kira ga wadanda aka zaba da su bi ka’idoji da sharuddan yarjejeniya da za su sanya hannu. An kuma shawarce su da su cika sharuddan da za a fayyace a cikin yarjejeniyoyin domin NCAA a shirye take ta sanya takunkumin karya doka. 

Ya koka da batun jinkiri da soke jigilar jiragen sama kamar yadda aka samu a shekarar da ta gabata, yana mai bayyana hakan a matsayin mai yin tasiri a dukkan ayyukan da ma ya shafi ayyukan Saudiyya ma. A kan wannan cikas na dindindin, tun da farko Hukumar Kula da Sufurin Jiragen Sama (GACA) ta gayyaci NCAA don auna irin tasirin da take da shi a ayyukan Hajjin filayen jiragen sama na Madina da Jeddah. Don haka, NCAA ta ɗora tsauraran matakai don guje wa sokewa da jinkirin tashin jirgin a wannan shekara.
 
Kaftin Nuhu da sauran masu jawabi a wurin taron sun bayyana damuwarsu kan rufe sararin samaniyar Sudan sakamakon yakin da ake yi a kasar. An bayyana cewa alhazai na iya yin tafiyar sa'o'i bakwai da rabi a kowace tafiya saboda yiwuwar sauya hanya.
 
A wani labarin kuma hudu daga cikin biyar din da aka zaba domin gudanar da jigilar daukar alhazai, sun bukaci karin lokaci kafin sanya hannu kan yarjejeniyar. Dukkansu  kamfanonin jiragen sama ne na cikin gida. 

A cewar ma’aikatan jirgin, akwai bukatar su ci gaba da tuntubar juna da yin lissafin kafin su koma tattaunawa da hukumar ta NAHCON don bayyana amincewarsu ta karshe zuwa ranar Talata 9 ga watan Mayu. 

Sai dai kamfanin FlyNas na Saudiyya ya rattaba hannu tare da nuna shirin fara jigilar Hajji na 2023. Don haka, an ci gaba da ci gaba da aiwatar da tsarin jigilar jirgin tare da FlyNas.
 
Tawagar farko ta aikin Hajji na 2023 da ta kunshi zababbun ma’aikatan NAHCON da ma’aikatan lafiya kadan ne ake sa ran za su bar kasar nan da ranar 21 ga Mayu, 2023.

Kotu ta ɗaure Ekweremadu shekara tara a gidan yari

An yanke wa wani hamshaƙin ɗan siyasar Najeriya, Ike Ekweremadu, da mai ɗakinsa, hukuncin ɗauri a gidan yari bayan kotu a Birtaniya ta same su da laifi kan yunƙurin safarar sassan jikin ɗan'adam.

Kotun ta yanke musu hukuncin ne tare da wani likita "mai shigar musu tsakani" bayan sun kai wani matashi Birtaniya daga Lagos.

Yanzu dai, Sanata Ike Ekweremadu zai shafe kusan shekara goma a gidan yarin Birtaniya.

Sanatan mai shekara 60, da mai ɗakinsa Beatrice 'yar shekara 56, sun so a cire wa matashin sashen jikinsa ne da nufin dasa wa 'yarsu Sonia 'yar shekara 25, kamar yadda ma'auratan suka bayyana wa Kotun Old Bailey
An kuma samu "mai shiga tsakani" Dr Obinna Obeta da matar sanata Ekweremadu, Beatrice, da laifi

Tun da farko kotu ta samu ma'auratan da likita Dr Obinna Obeta, mai shekara 50, da laifin haɗa baki don ci da gumin mutumin ta hanyar cire ƙodarsa.

Ita ce shari'a ta farko a ƙarƙashin dokokin haramta bautar zamani.

Yadda aka kama Sanatan Najeriya bisa zargin yunkurin cire sassan jikin mutum
24 Yuni 2022
Kotu ta samu Ekweremadu da laifin yunƙurin safarar sassan ɗan adam
23 Maris 2023
Matashin da aka yi yunƙurin cire wa ƙoda domin bai wa ƴar Ekweremadu
25 Maris 2023
Ike Ekweremadu, wanda alƙalin kotun ya bayyana a matsayin "jigon da ya shirya abin da ya faru gaba ɗaya", zai yi zaman gidan yari tsawon shekara tara da wata takwas.

Hkaa kuma ta yanke wa Dr Obinna Obeta hukuncin ɗaurin shekara 10 bayan alƙalin ya gano cewa shi ne ya samo mutumin da zai ba da gudunmawar wanda matashi ne talaka, kuma mai rauni.

Ita kuma matar sanatan na Najeriya, Beatrice Ekweremadu an yanke mata hukuncin ɗaurin shekara huɗu da wata shida saboda yadda ta ɗan sa hannu wajen aikata laifin.

A wani zaman yanke hukunci da aka nuna ta talbijin, Mai shari'a Justice Johnson ya nunar cewa Ike Ekweremadu, mutum ne da "ƙimarsa ta yi matuƙar zubewa".

Ya ce: "Masu fasa-ƙwaurin mutane a tsakanin ƙasashen duniya don cire sassa jikin mutum, abin da suke aikatawa wani nau'in bautar da ɗan'adam ne."

Mutumin da suka yi safarar tasa, wani talaka ne mai sana'ar tireda a Lagos, da suka kai shi Birtaniya don a cire masa ƙoda guda ɗaya, da nufin dasa wa 'yar Ekweremadu.

Ya dai tsere ne saboda tsoron mutuwa, inda ya kai kansa ofishin 'yan sanda kimanin shekara ɗaya da ta wuce kuma ya ba da rahoton abin da ya faru, bayan asibitin Royal Free Hospital ya nemi a dakatar da aikin da aka tsara yi a kan kuɗi £80,000.
BBC 

Thursday, 4 May 2023

Wani Yaro Ya Kashe Mahaifiyarsa A Kano

Wani karamin yaro a unguwar Rimin Kebe da ke Karamar Hukumar Nassarawa a Jihar Kano ya daba wa mahaifiyarsa wuka lamarin da ya sa ta ce ga garinku nan.

Wani ganau mazaunin yankin, Muhammad Abdu, ya shaida wa Aminiya cewa lamarin ya faru ne yayin da aka sami jayayya tsakanin marigayiyar da dan nata da ake wa lakabi da Kwarangwal.


Ya bayyana cewa, “lokacin da muka ji ihunta mun garzaya gidan don kai dauki inda muka same ta kwace cikin jini male-male ga kuma yanka a jikinta.”

A cewarsa tuni wanda ake zargi ya cika wandonsa da iska bayan ya yi aika-aikar.

Haka kuma ya bayyana cewa daga baya an garzaya da marigayiyar Asibitin Koyarwa na Muhammadu Abdullahi Wase.

Kakakin Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ya tabbatar da faruwar lamarin a ranar Alhamis, inda ya ce zai yi karin haske akan lamarin daga bisani.
AMINIYA 

Rano Air Zai Fara Aiki Ranar Lahadi

Daya daga cikin sabbin kamfanonin jiragen sama a kasar, Rano Air, ya ce zai fara aikin zirga-zirga a ranar Lahadi, 7 ga Mayu, 2023.

Kamfanin jirgin wanda ya bayyana hakan a wata sanarwa da ya fitar a shafinsa na Twitter ranar Alhamis, ya ce gwamnan jihar Kano, Abdullahi Ganduje, zai kaddamar da jirgin da zai tashi daga filin jirgin sama na Aminu Kano.

Hukumar gudanarwar kamfanin na Rano Air na sanar da al’umma cewa gwamnan jihar Kano Dr. Umar Abdullahi Ganduje zai tashi da jirgin a ranar Lahadi 7 ga watan Mayu, 2023 a tashar jirgin kasa ta Malam Aminu Kano. Kano karfe 10:00 na safe. Jirgin kasuwanci na Abuja da Kano zuwa garuruwa daban-daban na Najeriya za su fara aiki nan take."

Jaridar PlatinumPost ta rawaito cewa Rano Air mallakin hamshakin attajirin dan kasuwa ne kuma hamshakin mai kasuwanci Man Fetur dan asalin Kano, Auwalu Rano, shi ne Shugaban Rukunin kamfanin A.A. Rano.

Kamfanin jirgin, wanda aka kafa a shekarar 2019, ya samu lambobi biyar na EMB 145, kuma yana aiki a Abuja.


Labari Cikin Hotuna : Kamfanin Flynas Ya sanya Hannu kan Yarjejeniyar Jigilar Alhazan Najeriya

Kamfanin Flynas dake kasar Saudiyya ya sanya hannu kan yarjejeniyar dibar maniyyata aikin Hajin bana

An gudanar da taron sanya hannun ne a hedikwatar hukumar alhazai ta kasa NAHCON dake babban birnin tarayya Abuja

Saudiyya Ta Yi Wa Messi Tayin Ninkin Albashin Ronaldo

 


Kungiyoyin kwallon kafa a kasar Saudiyya na zawarcin gwarzon dan wasan duniya, Lionel Messi, na kungiyar PSG, da tayin albashin da ya zarce na kowane dan wasa a duniya.

Rahotanni sun nuna cewa wata kungiya da ke zawarcin Messi a Saudiyya ta yi masa tayin albashin Naira biliyan 183.5 (Dala miliyan 400) a shekara, idan kwantaraginsa ya kare da PSG a wata mai zuwa.

Kafar labarai ta Telegraph ta kasar Birtaniya ta ce dan wasan ya fara tunanin duba tayin kuma tuni kungiyar ta fara tattaunawa da Kyaftin din na kasar Argentina kan kwangilar da take masa tayi, bayan dakatarwar da PSG ta yi masa.

Idan hakan ta tabbata, Messi zai rika karbar kusan ninki biyun albashin babban abokin hamayarsa Cristiano Ronaldo, wanda a halin yanzu Al Nassr ta kasar Saudiyya ke biyan sa Naira biliyan 96.3 Dala miliyan 210 a shekara, zuwa 2025.

Wannan sabuwar ta taso ne bayan da kungiyar PSG ta dakatar da Messi na tsawon mako biyu ba tare da albashi ba, saboda wata ziyara da ya kai Saudiyya ba da izinin kungiyar ba.

A baya dai an yi ta rade-radin kungiyar Al Hilal ta Saudiyya ce ke neman daukar Messi, daga baya da PSG ta takatar da shi kuma maganar ta kara tasowa.

AMINIYA

Hajj2023: Hukumar NAHCON Ta Kaddamar Da Babban Kwamitin Kwamitin Tsaro

A wani yunkuri na karfafa matakan tsaro da tabbatar da tsaron alhazan Najeriya, shugaban hukumar alhazai ta kasa (NAHCON) Alhaji Zikrullah Kunle Hassan ya kaddamar da kwamitin tsaro na kasa (CSC) a hedikwatar hukumar a ranar Alhamis. 
Kwamitin wanda ya kunshi wakilai daga hukumomin tsaro daban-daban da suka hada da rundunar ‘yan sandan Najeriya da jami’an tsaron farin kaya da jami’an tsaron farin kaya da ma’aikatan gwamnati da hukumar shige da fice ta kasa da dai sauransu, an dora musu alhakin tabbatar da tsaron. Alhazan Najeriya a lokacin aikin Hajjin bana mai zuwa.
A yayin bikin kaddamar da Kwamitin, shugaban NAHCON ya jaddada muhimmancin tsaro a aikin Hajji. Ya kuma jaddada bukatar hada hannu wuri guda domin tabbatar da tsaron alhazai.
Ahmad Mu'azu 
(NAHCON) 

Ganduje Ya Kaddamar Da Sabbin Tituna Hudu A Jihar Kano

Hotunan sabbin tituna guda hudu wanda Mai Girma Gwamnan Jihar Kano Dr Abdullahi Umar Ganduje OFR ya gina kuma ya kaddamar a jiya Laraba.

Sabbin titunan da kuma wandanda aka sabunta sun hada da:

i) Sheikh Mahmud Salga Road dake karamar hukumar Dala

ii) Ahmadu Bello Way dake Karamar Hukumar Nassarawa 

iii) Gash Road dake Karamar Hukumar Nassarawa 

iv) Kwanar Akuya Road dake Karamar Hukumar Fagge wanda ya Kare a wani bangare na Karamar Hukumar Ungoggo.

A jawabinsa Mai Girma Gwamnan ya bayyana aniyarsa ta cigaba da bude irin wadannan ayyukan alkhairi na raya kasa da bunkasa kasuwanci har zuwa yan kwanakin da suka rage masa akan mulki.

SSA Photography 

Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

SAPZ Kano partners ABCOAD to organize FFS Training for Youth and Women.

The Special Agro-Industrial Processing Zones (SAPZ) Programme, Kano State, in collaboration with Audu Bako College of Agricultur...