Gwamna Yusuf ya aika sunan Murtala Garo zuwa Majalisar Dokoki domin Tantance Shi A Matsayin Mataimakinsa

Gwamnan Jihar Kano, Abba Kabir Yusuf, ya aika sunan Alhaji Murtala Sule Garo zuwa Majalisar Dokokin Jihar domin tantance shi tare da amincewa da shi a matsayin Mataimakin Gwamna.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa da Babban Sakataren Yada Labaran Gwamnan, Mustapha Muhammad, ya sanya wa hannu.

Nadin ya yi daidai da Sashe na 191(3) na Kundin Tsarin Mulkin Najeriya na 1999 (wanda aka yi wa kwaskwarima), wanda ke bai wa Gwamna damar nada Mataimakin Gwamna idan mukamin ya zama babu kowa a ciki.

Mukamin ya zama babu kowa ne bayan murabus din da tsohon Mataimakin Gwamna, Abdussalam Gwarzo, ya yi da kansa a ranar 27 ga Maris, 2026.

Bayan yin tuntuba mai fadi da masu ruwa da tsaki, Gwamnan ya bukaci Majalisar da ta amince da nadin Murtala Sule Garo.

Murtala Sule Garo mai shekaru 48, gogaggen dan siyasa ne kuma mai kwarewa a harkokin gudanarwa, inda ya shafe sama da shekaru ashirin yana rike mukamai daban-daban na zabe da na nada.

Ya taba zama Sakataren Tsare-tsare na jam’iyyarsa a jihar, Mashawarcin Gwamna na Musamman, da kuma zababben Shugaban Karamar Hukumar Kabo.

Haka kuma ya taba zama Shugaban ALGON a Kano, Kwamishinan Kananan Hukumomi da Harkokin Sarauta, da kuma dan takarar Mataimakin Gwamna na jam’iyyar APC a zaben 2023.

Nadin nasa wani bangare ne na kokarin kara inganta shugabanci da kuma dorewar kyakkyawan aikin yi wa al’umma hidima a Jihar Kano.

Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki