Gwamnatin Kano Ta Bayar Da Hutun Bikin Takutaha

Gwamnan jihar Kano Alhaji Abba Kabir Yusuf ya ayyana yau Laraba 4 ga Oktoba, 2023 a matsayin ranar hutu domin tunawa da haihuwar fiyayyen halitta Annabi Muhammad tsira da amincin Allah su tabbata a gare shi.

A Cikin sanarwar da Kwamishinan yada labarai na Kano, Injiniya Abba Malam Baba Halilu Dantiye ya sanyawa hannu, Gwamnan ya bukaci al’ummar jihar da su yi amfani da lokutan bukukuwa domin yin tunani a kan koyarwar Manzon Allah Sallallahu Alaihi Wasallama da sanya su cikin harkokinsu na yau da kullum.

Ya kuma bukaci jama’a da su rika yin addu’a domin samun zaman lafiya da ci gaba a Kano a Najeriya baki daya.

Ya yi addu’ar Allah ya ganar damu wannan lokaci mai wuya, ya kuma sa mu dace a wannan damina da kuma damina mai zuwa.


Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki