Search This Blog

Wednesday, 4 October 2023

Yanzu-yanzu: Gwamnan Kano ya yi sabbin nade-naden mukaman shugabannin ma'aikatun gwamnati

A bisa kokarin sanya hannun da suka dace don inganta shugabanci na gari, Gwamna Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin shugabannin hukumomin na jihar nan take.

A sanarwar da babban sakataren yada labaran Gwamnan, Sanusi Bature Dawakin Tofa ya sanyawa hannu, yace Wadanda aka nada sune kamar haka.

1. Salisu A. Kabo, Darakta Janar na hukumar Kula da ci gaban matasa

2. Dr. Hamisu Sadi Ali, Darakta Janar na ofishin kula da basussuka

3. Abduljabbar Mohammed Umar, Darakta Janar na KAN-INVEST

4. Yusuf Kabir Gaya, Shugaban Hukumar SUBEB

5. Mustapha Adamu Indabawa, Manajan Daraktan Gidan Talabijin na Abubakar Rimi (ARTV)

6. Hamisu Dogon Nama, Manajan Daraktan Kasuwar Kantin Kwari

7. Abdulkadir B. Hussain, Manajan Daraktan Kasuwar Sabon Gari

8. Dr Kabiru Sani Magashi, Mukaddashin Manajin Darakta na KASCO

9. Aminu Aminu Mai-Famfo, Mataimakin Manajin Darakta na KASCO

10. Engr, Abubakar Sadiq J. Mataimakin Manajin Darakta Hukumar sufuri ta  Kano Line

Gwamnan ya umarci wadanda aka nada da su yi amfani da kwarewarsu wajen gudanar da ayyukansu ta yadda za su yi wa al’ummar jihar hidima da kuma tabbatar da amincewar da aka yi musu.


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

FG Urges KOICA, FAO to Align Agricultural Intervention with Nigeria’s Development Priorities, Ward-Based Strategy

The Federal Government has called for stronger alignment between development partners’ interventions and Nigeria’s national deve...