Gobara ta tashi a Kotun Kolin Najeriya

Zuwa yanzu dai ba a kai ga gano musabbabin tashin gobarar ba, amma majiyarmu ta ce jami’an hukumar kashe gobara sun isa harabar kotun.

Wannan na daga cikin gobarar da aka samu a manyan cibiyoyin gwamnati a Babban Birnin Tarayya, Abuja.

A watan Mayun 2023 gobara ta lakume wani yanki na barikin sojojin sama da ke Abuja.


A cikin watan ne aka yi gobara a ginin Hukumar Akwatin Gidan Waya (NIPOST) a Abujar.

A watan Afrilu Ofishin Akanta-Janar na Kasa (AGF) ya yi gobara.
(AMINIYA)


Popular posts from this blog

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele

Zababben Gwamnan Kano Ya Kafa Kwamitin Karbar Mulki