Search This Blog

Wednesday, 1 February 2023

Shugaban Hukumar NAHCON Ya Karbi Sabon Kwamishinan Kudu Maso Gabas

Dokta Afikpo ya zama Kwamishinan NAHCON ne bayan rasuwar wakilin shiyyar siyasa, Alhaji Ibrahim Ogbonnia Amah, a ranar 30 ga watan Nuwamba, shekarar da ta gabata.

Shugaban Hukumar Alhazai ta Najeriya (NAHCON), Alhaji Zikrullah Kunle Hassan a ranar Laraba ya karbi bakuncin sabon kwamishinan hukumar da ke wakiltar Kudu maso Gabas, Dr Sulaiman Afikpo.

Dokta Afikpo ya zama Kwamishinan NAHCON ne bayan rasuwar wakilin shiyyar siyasa, Alhaji Ibrahim Ogbonnia Amah, a ranar 30 ga watan Nuwamba, shekarar da ta gabata.

Hisbah Ta Wanke Matar Da Ta Auri Saurayin ’Yarta A Kano Daga Zargi

 


Kwamitin da Hukumar Hisbah ta Jihar Kano ta kafa kan binciken auren matar da ta auri saurayin ’yarta, ya wanke ta daga zarge-zargen da ake mata.

Wannan na cikin wata sanarwa da kakakin hukumar, Alhaji Lawan Ibrahim ya fitar a Kano a ranar Talata.

Sanarwar ta ce “Gabatar da rahoton binciken da kwamiti ya ya yi karkashin jagorancin Kwamanda Malam Hussain Ahmed, an gano auren halal ta yi kuma ta cika duk wasu sharuda da addini ya tanadar.”

Sanarwar ta kuma ce bincikensu ya nuna cewar matar mijinta ya sake ta tun da fari kuma ta yi iddar wata uku kamar yadda addinin Musulunci ya tsara, kafin daga bisani ta auri saurayin ’yarta da ta daina so.

Mataimakin Kwamandan ya yi watsi da zargin da ake wa matar na cewar ita ta kashe aurenta don ta auri saurayin ’yarta.

“Auren halal suka yi kamar yadda Musulunci ya tsara, shi ya sa Kwamandan Hisbah a Karamar Hukumar Rano ya jagoranci daurin auren.”

Babban Kwamandan Hukumar Hisbah na Jihar, Harun Ibn-Sina, ya jinjina wa kwamitin kan yadda suka gudanar da bincike tare da gudanar da aikinsu kan lamarin

Ibn Sina ya ce hukumar ta yi nazari ntsanaki wajen zabar mambobin kwamitin duba da tarin iliminsu na Addini da kuma gogewa wajen warware matsalolin zamantakewa

Ya gargadi jama’a da su guji yada labaran karya da fadar abin da ba su sani ba game da Musulunci.

Ya kuma bukaci al’umma da suke neman ilimi, domin Addinin Musulunci ya yi tanadin komai game da aure da abin da ya shafi iyali.

Tun da farko, Aminiya ta ruwaito yadda matar ta auri saurayin ‘yarta, wanda hakan ya sa mutane suka dinga tofa albarkacin bakinsu.

Wasu da dama sun yi Allah wadai da halin matar kan aure saurayin da diyarta ta yi soyayya da shi

(AMINIYA)

rai

Tuesday, 31 January 2023

Muna Kan Tataunawa Da Kwankwaso Da Obi - Atiku

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Atiku Abubakar ya bayyana cewa yana tattaunawa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigerian People Party (NNPP) Rabi’u Musa Kwankwaso domin samun goyon baya da hadin gwiwa.

A wata hira da BBC Hausa, Atiku ya ce yana kuma tattaunawa da dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party (LP), Peter Obi.

Ya ce ‘yan biyun Obi da Kwankwaso ba su da wata barazana ga damarsa a zaben.

“Ban ga wata barazana domin ba ma tare da su (Kwankwaso da Obi). Muna cikin tattaunawa da su, watakila daya daga cikinsu ya zo,” inji shi.

Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP Atiku Abubakar ya bayyana cewa yana tattaunawa da dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar New Nigerian People Party (NNPP) Rabi’u Musa Kwankwaso domin samun goyon baya da hadin gwiwa.

A wata hira da BBC Hausa, Atiku ya ce yana kuma tattaunawa da dan takarar shugaban kasa na jam'iyyar Labour Party (LP), Peter Obi.

Ya ce ‘yan biyun Obi da Kwankwaso ba su da wata barazana ga damarsa a zaben.

“Ban ga wata barazana domin ba ma tare da su (Kwankwaso da Obi). Muna cikin tattaunawa da su, watakila daya daga cikinsu ya zo,” inji shi.

Dangane da Rikicin PDP da ya addabe Atiku, ya ce, “Kowace jam’iyya na da rikicin cikin gida, muna tattaunawa da su. Yawancin ba a PDP ba ne ko kuma a wasu jam'iyyu kuma tabbas hakan ba zai sa mu fadi zabe ba saboda muna shirye-shiryen zabe a yanzu.

“Zaben da ake yi a yanzu ba kamar a baya ba ne lokacin da gwamna zai zabi wanda zai zaba, zaben yau yana hannun masu zabe.”

Dan takarar shugaban kasar ya kuma yi alkawarin bude dukkan iyakokin Najeriya idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa.

Dangane da Rikicin PDP da ya addabe Atiku, ya ce, “Kowace jam’iyya na da rikicin cikin gida, muna tattaunawa da su. Yawancin ba a PDP ba ne ko kuma a wasu jam'iyyu kuma tabbas hakan ba zai sa mu fadi zabe ba saboda muna shirye-shiryen zabe a yanzu.

“Zaben da ake yi a yanzu ba kamar a baya ba ne lokacin da gwamna zai zabi wanda zai zaba, zaben yau yana hannun masu zabe.”

Dan takarar shugaban kasar ya kuma yi alkawarin bude dukkan iyakokin Najeriya idan aka zabe shi a matsayin shugaban kasa.

Karon Farko A 2023 Sanata Rabi'u Musa Kwankwaso Ya Bayyana Babu Jar Hula

A karon farko tsohon gwamnan jihar Kano kuma dan takarar shugabancin Najeriya a jam’iyyar NNPP, Senata Rabi’u Musa Kwankwaso ya bayyana babu jar hula.

Sanata Rabi’u Kwankwaso ya bayyana cikin shigar Yarabawa a gangamin yakin neman zaɓensa na shugaban kasa da sauran yan takarkari a shiyyar kudu masu yammacin Najeriya da ya gudana a birnin Oyo da ke jihar Ibadan.

Dantakarar shugabancin Najeriya a jam’iyyar NNPP, Senata Rabi’u Kwankwaso da sauran jiga- jigan jam’iyyar
A lokacin gangamin yakin neman zaben Senata Kwankwaso ya bukaci al’ummar jihar Ibadan da su zabi jam’iyyar NNPP a matakin kasa da jiha.

Sanya jar hular dai wata alamace ta mabiya tsagin Kwankwasiyya – da ke goyon bayan tsohon gwamna Rabi’u Musa Kwankwaso.

Turawa Abokai
Labarai24

Sarkin Dutse Alhaji Nuhu Muhammad Sunusi ya Rasu

Marigayi Mai Martaba Dokta Nuhu Muhammadu Sanusi shi ne basaraken gargajiya mai ajin farko (Sarki) na Dutse babban birnin jihar Jigawa a yankin Arewa maso yammacin Najeriya. Sannan kuma shi ne Shugaban Jami’ar Jihar Sakkwato.

Sarki Sanusi shine jagoran masu fafutukar kare gandun daji da kuma koren halittu a fadin masarautarsa

Wannan alƙawarin rage tasirin sauyin yanayi ne ya sa ya gina filin wasan Golf na Dutse wanda ake kyautata zaton na ɗaya daga cikin mafi girma a Najeriya da ke da ciyayi masu  masu yawa da namun daji.

Kafin ya hau karagar mulki, Dr. Sanusi ya samu gogewa sosai a fannin tuntubar juna a fannin noma da sarrafa sarkakkun ayyukan masana'antu a nahiyoyi. Baya ga sha'awar tafiye-tafiye, Sarki Sanusi ya gabatar da kasidu a tarurrukan karawa juna sani na kasa da kasa, kuma ya rubuta litattafai da dama, ciki har da tarihin rayuwarsa da kuma tarihin Dutse mai zurfi.

A karkashin mulkinsa, Masarautar Dutse na rikidewa d zuwa samun ci gaba inda al'umar yankin ke da himma wajen tinkarar kwararowar hamada da kuma dabi’ar kyautata muhalli. Ya kafa makarantu masu zaman kansu da dama ga matasa da manya kuma ya karfafa wa al’umma gwiwa da su nemi ilimi a matsayin babban makamin ci gaba da dorewar muhalli.

Sarki Dr Nuhu Sanusi ya samu digirin farko da na biyu a jami’ar Ohio ta kasar Amurka a shekarar 1972 da 1974, sannan ya samu digiri na biyu a jami’ar Bradford ta kasar Birtaniya a shekarar 1977. An zabe shi dan majalisar dokokin Najeriya a 1989 kuma ya samu lambar yabo ta kasa mai martaba. karrama kwamandan oda na Niger, CON, baya ga karramawar digirin digirgir da Jami’ar Fasaha ta Tarayya da ke Owerri ta Jihar Imo ta yi.

Yanzu - Yanzu: Bankuna Zasu Karbi Tsofaffin Kudi Ko da Bayan Karewar Wa'adi - Emefiele


Gwamnan Babban Bankin Najeriya, Godwin Emefiele, ya ce Bankuna za su ci gaba da karbar tsoffin takardun kudi na Naira ko da bayan wa’adin musaya da sabbin takardun kudin da aka zayyana.

Idan dai za a iya tunawa, a kwanakin baya ne babban bankin ya kara wa’adin canza shekar kudi naira 1,000 da naira 500 da kuma N200, biyo bayan korafin ‘yan Najeriya.

Sai dai a yayin da shugaban na CBN ya bayyana a gaban kwamitin majalisar wakilai kan sabon tsarin sauya fasalin Naira da kuma canjin naira a ranar Talata, shugaban na CBN ya ce har yanzu bankuna za su karbi tsoffin takardun bayan wa’adin.

Emefiele ya ce idan aka yi la’akari da sashe na 20, karamin sashe na 3 na dokar CBN ta shekarar 2007, ko da tsofaffin kudaden sun rasa matsayinsu na neman kudi, CBN za ta ci gaba da karbar tsofaffin takardun kudi.

Mista Emefiele ya ce dole ne bankunan kasuwanci su karbi kudin ko da bayan wa'adin 10 ga watan Fabrairu

(SOLACEBASE) 

A Karhse Dai Emefiele Ya Bayyana A Gaban Kwamitin Majalisar Wakilai Kan Batun Sababbin Kudi

A ranar Talata ne gwamnan babban bankin Najeriya Godwin Emefiele ya gurfana gaban kwamitin majalisar wakilai, inda suke binciken yadda aka yi musanya da Naira.

A halin yanzu dai kwamitin da tawagar CBN na gudanar da taro a majalisar dokokin kasar.

An fara taron ne da misalin karfe 12:05 na rana bayan shafe sama da awa daya a sirrance.

Idan dai za a iya tunawa majalisar da kwamitin sun yi barazanar kama wasu da dama a ranar Alhamis bayan Mista Emefiele ya kauracewa majalisar.

Shugaban bankin na CBN ya sanar da tsawaita wa’adin canza canjin kudin zuwa ranar 10 ga watan Fabrairu. Sai dai kwamitin ya dage cewa dole ne Emefiele ya bayyana a gabansu.

A lokacin da aka fara taron, Shugaban Kwamitin, Ado Doguwa ya ce shugaban CBN ya bayar da dalilan rashin amsa gayyata a baya.

Cikakken labarin zai zo muku nan gaba kadan 

SOLACEBASE 

Monday, 30 January 2023

Buhari ya yi kira ga 'yan Najeriya su riƙa gode wa Allah

 


Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya ce abubuwan more rayuwa da ake ginawa a faɗin ƙasar 'abin ban sha'awa' ne.

A wata sanarwa mai mai magana da yawun shugaban ƙasar Femi Adesina ya fitar, Shugaba Buhari ya yi kira ga 'yan ƙasar da su riƙa yaba wa da abubuwan more rayuwa da ake gina musu, la'akari da yanayin da ƙasar ke ciki idan an kwatanta da sauran ƙasashe.

Shugaban na jawabi ne a lokacin da yake kammala ziyarar aiki ta yini guda da ya kai jihar Kano da ke arewacin ƙasar domin ƙaddamar da wasu ayyukan da gwamnatin jihar da ta tarayya da kuma wasu kamfanoni masu zaman kansu suka yi.

Shugaban ya ce ‘‘muna da ƙasaitacciyar ƙasa, amma ba ma yaba mata, har sai mun ziyarci ƙasashe maƙwabta da sauran ƙasashe, inda sai mutane sun yi da gaske sannan su sami abinci sau ɗaya a rana''.

‘‘A lokacin da nake shawagi a cikin jirgi adadin dogayen gine-ginen da na gani da yawan ci gaban da ake da shi a doron ƙasa abin ' ban sha'awa' ne. Mun gode wa Allah, Mun gode wa Allah'', in ji Buhari.

Shugaban ƙasar ya kuma umarci manyan 'yan ƙasar da su ƙarfafa wa matasa gwiwwa wajen rungumar ilimi, yana mai cewa dole ko ana so, ko ba a so makomar ƙasar a hannun matasan take.

Ya ce '‘dole su rungumi ilimi, Fasaha ta saukaka abubuwa da dama, to amma babu abin da zai maye gurbin ilimi, dan Allah ku ƙarfafa wa yara gwiwwa su samu ilimi''.

Shugaban ya kuma jinjina wa gwamnan jihar Abdullahi Umar Ganduje bisa ayyukan raya jihar da ya shimfiɗa, yana mai cewa a ziyarar baya-bayan nan da ya kai jihohin Kogi da Yobe da Legas da Katsina ya nuna cewa, gwamnonin waɗannan jihohi sun yi namijin ƙoƙari, wajen yin ayyukan raya ƙasa a jihohin nasu idan aka kwatanta da kuɗaden da suke samu.

(BBC)

Sunday, 29 January 2023

Shugaba Buhari Zai Zo Kano Gobe Don ƙaddamar da ayyuka Guda 8



Gwamnatin jihar Kano ta ce ta kammala shirye-shiryen tarbar shugaban kasa Muhammadu Buhari da zai kai ziyarar aiki domin kaddamar da ayyukan raya kasa guda takwas a jihar.
Wata sanarwa da kwamishinan yada labarai da harkokin cikin gida, Malam Muhammad Garba ya fitar ta ce gwamna Abdullahi Umar Ganduje zai karbi bakuncin shugaban kasar da mukarrabansa.
Ya ce yayin da yake Kano, Buhari zai kaddamar da aikin tashar wutar lantarki mai amfani da hasken rana mai karfin megawatt 10, Kano a tashar tsandauri ta Dala Inland Dry Port na biliyoyin naira a Zawachiki, karamar hukumar Kumbotso.
Sauran ayyukan sun hada da cibiyar ajiye bayanai ta jihar Kano da ke Audu Bako Secretariat Data da harabar ofis da ke Galaxy Backbone Limited Project a Ahmadu Bello Way.
Sauran kuma an ba da aikin cibiyar kula da cutar daji a asibitin kwararru na Muhammadu Buhari, Giginyu; Gada Mai musayar hannu ta Muhammadu Buhari a Hotoro kan titin Maiduguri da Cibiyar koyar da sana'o'i ta bAliko Dangote dake kan titin Zaria da Rukunin Gidajen Gwamnatin Tarayya dake Gandun Sarki, Darmanawa.

Da dumi-dumi: CBN ta kara wa’adin karbar tsofaffin kuɗin




 A karshe dai babban bankin Najeriya CBN ya kara wa’adin daina karɓar tsofaffin kudi har zuwa nan da kwanaki 10.

 
Majiyarmu ta rawaito a wata sanarwa da gwamnan babban bankin na CBN, Godwin Emefiele ya fitar a ranar Lahadi, ya ce sabon wa’adin zai kare ne 10 ga watan Fabrairun 2023.

Duk da haka, har yanzu ’yan Najeriya za su iya mika tsofaffin takardun Kudinsu kai tsaye zuwa bankin CBN har nan da ranar 17 ga Fabrairu, 2023.

 
Talla daukar nauyi Suraj Umar Wudil
‘Yan Najeriya dai sun yi ta kokawa kan rashin wadatattun sabbin kudin wanda da farko aka ce wa’adin zai kare a ranar 31 ga watan Janairu .

A baya dai CBN ta ce ba za ta kara wa’adin ba.

 


Kada Ku Nemi Na Saki 'Yan Daba - Muhuyi Magaji Ya Gargadi 'Yan Siyasa

Presidential delegation pays condolence visit to Hamza Darma’s family in Kano

A high-powered presidential delegation has paid a condolence visit to the family of late Alhaji Hamza Usman Darma, a prominent K...